• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tsaro

A ƙoƙarin tabbatar da tsaro a iyakokin ƙasa da magance aikata lailufa a iyakokin ƙasar nan, Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye zaratan jami’ai mata masu ɗaukar makami a karon farko da ta horar domin gudanar da aiki na musamman.

Da yake gabatar da jawabi wajen faretin yaye jami’ai matan guda 61 a ranar Juma’a, Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya bayyana cewa babban aikin hukumar shi ne samar da tsaro a iyakokin ƙasa domin ƙarfafa tsaron cikin gida.

  • Aisha Buhari Ta Janye Kara Kan Aminu Mohammed Da Ya Ce Ta Yi ‘Bulbul’

 

“A wannan biki na yau, rana ce ta ƙarfafa mana giwa na ƙoƙarin tabbatar da cewa mun tsare iyakokinmu da rayuka da dokiyoyin mutanenmu.

“Hukumar NIS tana da muhimmiyar rawa da take takawa wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, laifukan iyakoki da kuma sauran duk wata barazanar tsaro da ke fuskantar ƙasarmu. Domin ƙara ƙarfafa abubuwan da muka daɗe muna gudanarwa na tsawon lokuta, shugabancina ya mayar da hankali ne kan wasu ɓangarori guda uku waɗanda suka hada da: Kula da jin daɗin jami’anmu, gudanar da aiki ba tare da jinkiri ba da kuma inganta aiki irin wanda ake yi a ƙasashen da suka ci gaba a duniya wajen tabbatar da tsare iyakokin ƙasarmu.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

“Bisa waɗannan ɓangarori da na lissafo, NIS a ƙarƙashin jagorancina, a ko da yaushe ina muhimmanta kyautata jin daɗin jami’ai da ba su horo a-kai-a-kai ta yadda za su iya fuskantar ƙalubale daban-daban da ƙasarmu ke fuskanta. Za mu ci gaba da bayar da horo da sauran wasu shirye-shirye masu muhimmanci a gida da kumą ƙasashen ƙetare domin ƙara samun ilimi da shirya jami’anmu ta yadda za su iya sauke nauyin da ke kansu.”

Jere ya ƙara da cewa wanna biki wani mataki ne da zai ƙara kwazon aikin hukumar wajen inganta ayyukan jami’a a yankunan da ke fama da rashin tsaro a wurin gudanar da ayyukan ƙasa kamar yadda ake buƙata a lokaci bayan lokaci.

Ya ce waɗannan jami’ai guda 61 dukkansa mata ne waɗanda suka samu horon aiki kan yadda ake sarrafa makamai, kakkaɓo jirgi, tsaron iyakoki, yaƙar ‘yan ta’adda da sauran harkokin bincike da kuma horon sirri.

“Kamar yadda kuke iya gani a yau, waɗannan jami’ai sun nuna zimma tare da aiki kafanɗa da kafaɗa da maza wajen yi wa ƙasarmu hidima. Ina sanar muku da cewa a yanzu haka hukumar ta ɓullo da shirin horar da jami’ai sama da 1000 a makarantar bayar da horo da ke Kano da kuma makarantar horar da jami’an kwastom da ke Goron Dutse a Kano. Muhimmancin bayar da wannan horo shi ne, tabbatar da cewa jami’anmu sun samu ƙwarewa wajen fuskantar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasarmu da kuma yin kafaɗa da kafaɗa da takwarorinsu na duniya wajen gudanar da ayyukan shige da fice.

“A wannan gaɓa, ina taya murna ga kwamandan NITSA da ma’aikatansa bisa kafa tarihi a yau, gaskiyar magana ita ce, aiki ne na farkon wanda ya horar da waɗannan zaƙaƙuran jami’ai, da farko sun kasance kamar ba za su iya ba, lallai ka gudanar da gagarumin aiki wanda ka cancanci yabo, hukumar gudanarwa ta NIS tana alfahari da kai bisa jajircewa wajen gudanar da aiki.” In ji CGI Jere.

Ana sa rai waɗannan jami’ai mata su taimaka wa ƙarfafa tsaron iyakokin da za a tura su kamar yadda NIS ta ƙudurta bisa jagorancin

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.