ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Tsaro

A ƙoƙarin tabbatar da tsaro a iyakokin ƙasa da magance aikata lailufa a iyakokin ƙasar nan, Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye zaratan jami’ai mata masu ɗaukar makami a karon farko da ta horar domin gudanar da aiki na musamman.

Da yake gabatar da jawabi wajen faretin yaye jami’ai matan guda 61 a ranar Juma’a, Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya bayyana cewa babban aikin hukumar shi ne samar da tsaro a iyakokin ƙasa domin ƙarfafa tsaron cikin gida.

  • Aisha Buhari Ta Janye Kara Kan Aminu Mohammed Da Ya Ce Ta Yi ‘Bulbul’

 

ADVERTISEMENT

“A wannan biki na yau, rana ce ta ƙarfafa mana giwa na ƙoƙarin tabbatar da cewa mun tsare iyakokinmu da rayuka da dokiyoyin mutanenmu.

“Hukumar NIS tana da muhimmiyar rawa da take takawa wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, laifukan iyakoki da kuma sauran duk wata barazanar tsaro da ke fuskantar ƙasarmu. Domin ƙara ƙarfafa abubuwan da muka daɗe muna gudanarwa na tsawon lokuta, shugabancina ya mayar da hankali ne kan wasu ɓangarori guda uku waɗanda suka hada da: Kula da jin daɗin jami’anmu, gudanar da aiki ba tare da jinkiri ba da kuma inganta aiki irin wanda ake yi a ƙasashen da suka ci gaba a duniya wajen tabbatar da tsare iyakokin ƙasarmu.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

“Bisa waɗannan ɓangarori da na lissafo, NIS a ƙarƙashin jagorancina, a ko da yaushe ina muhimmanta kyautata jin daɗin jami’ai da ba su horo a-kai-a-kai ta yadda za su iya fuskantar ƙalubale daban-daban da ƙasarmu ke fuskanta. Za mu ci gaba da bayar da horo da sauran wasu shirye-shirye masu muhimmanci a gida da kumą ƙasashen ƙetare domin ƙara samun ilimi da shirya jami’anmu ta yadda za su iya sauke nauyin da ke kansu.”

Jere ya ƙara da cewa wanna biki wani mataki ne da zai ƙara kwazon aikin hukumar wajen inganta ayyukan jami’a a yankunan da ke fama da rashin tsaro a wurin gudanar da ayyukan ƙasa kamar yadda ake buƙata a lokaci bayan lokaci.

Ya ce waɗannan jami’ai guda 61 dukkansa mata ne waɗanda suka samu horon aiki kan yadda ake sarrafa makamai, kakkaɓo jirgi, tsaron iyakoki, yaƙar ‘yan ta’adda da sauran harkokin bincike da kuma horon sirri.

“Kamar yadda kuke iya gani a yau, waɗannan jami’ai sun nuna zimma tare da aiki kafanɗa da kafaɗa da maza wajen yi wa ƙasarmu hidima. Ina sanar muku da cewa a yanzu haka hukumar ta ɓullo da shirin horar da jami’ai sama da 1000 a makarantar bayar da horo da ke Kano da kuma makarantar horar da jami’an kwastom da ke Goron Dutse a Kano. Muhimmancin bayar da wannan horo shi ne, tabbatar da cewa jami’anmu sun samu ƙwarewa wajen fuskantar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasarmu da kuma yin kafaɗa da kafaɗa da takwarorinsu na duniya wajen gudanar da ayyukan shige da fice.

“A wannan gaɓa, ina taya murna ga kwamandan NITSA da ma’aikatansa bisa kafa tarihi a yau, gaskiyar magana ita ce, aiki ne na farkon wanda ya horar da waɗannan zaƙaƙuran jami’ai, da farko sun kasance kamar ba za su iya ba, lallai ka gudanar da gagarumin aiki wanda ka cancanci yabo, hukumar gudanarwa ta NIS tana alfahari da kai bisa jajircewa wajen gudanar da aiki.” In ji CGI Jere.

Ana sa rai waɗannan jami’ai mata su taimaka wa ƙarfafa tsaron iyakokin da za a tura su kamar yadda NIS ta ƙudurta bisa jagorancin

Tsaro
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.