ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Tsaro

A ƙoƙarin tabbatar da tsaro a iyakokin ƙasa da magance aikata lailufa a iyakokin ƙasar nan, Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye zaratan jami’ai mata masu ɗaukar makami a karon farko da ta horar domin gudanar da aiki na musamman.

Da yake gabatar da jawabi wajen faretin yaye jami’ai matan guda 61 a ranar Juma’a, Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya bayyana cewa babban aikin hukumar shi ne samar da tsaro a iyakokin ƙasa domin ƙarfafa tsaron cikin gida.

  • Aisha Buhari Ta Janye Kara Kan Aminu Mohammed Da Ya Ce Ta Yi ‘Bulbul’

 

ADVERTISEMENT

“A wannan biki na yau, rana ce ta ƙarfafa mana giwa na ƙoƙarin tabbatar da cewa mun tsare iyakokinmu da rayuka da dokiyoyin mutanenmu.

“Hukumar NIS tana da muhimmiyar rawa da take takawa wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, laifukan iyakoki da kuma sauran duk wata barazanar tsaro da ke fuskantar ƙasarmu. Domin ƙara ƙarfafa abubuwan da muka daɗe muna gudanarwa na tsawon lokuta, shugabancina ya mayar da hankali ne kan wasu ɓangarori guda uku waɗanda suka hada da: Kula da jin daɗin jami’anmu, gudanar da aiki ba tare da jinkiri ba da kuma inganta aiki irin wanda ake yi a ƙasashen da suka ci gaba a duniya wajen tabbatar da tsare iyakokin ƙasarmu.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Bisa waɗannan ɓangarori da na lissafo, NIS a ƙarƙashin jagorancina, a ko da yaushe ina muhimmanta kyautata jin daɗin jami’ai da ba su horo a-kai-a-kai ta yadda za su iya fuskantar ƙalubale daban-daban da ƙasarmu ke fuskanta. Za mu ci gaba da bayar da horo da sauran wasu shirye-shirye masu muhimmanci a gida da kumą ƙasashen ƙetare domin ƙara samun ilimi da shirya jami’anmu ta yadda za su iya sauke nauyin da ke kansu.”

Jere ya ƙara da cewa wanna biki wani mataki ne da zai ƙara kwazon aikin hukumar wajen inganta ayyukan jami’a a yankunan da ke fama da rashin tsaro a wurin gudanar da ayyukan ƙasa kamar yadda ake buƙata a lokaci bayan lokaci.

Ya ce waɗannan jami’ai guda 61 dukkansa mata ne waɗanda suka samu horon aiki kan yadda ake sarrafa makamai, kakkaɓo jirgi, tsaron iyakoki, yaƙar ‘yan ta’adda da sauran harkokin bincike da kuma horon sirri.

“Kamar yadda kuke iya gani a yau, waɗannan jami’ai sun nuna zimma tare da aiki kafanɗa da kafaɗa da maza wajen yi wa ƙasarmu hidima. Ina sanar muku da cewa a yanzu haka hukumar ta ɓullo da shirin horar da jami’ai sama da 1000 a makarantar bayar da horo da ke Kano da kuma makarantar horar da jami’an kwastom da ke Goron Dutse a Kano. Muhimmancin bayar da wannan horo shi ne, tabbatar da cewa jami’anmu sun samu ƙwarewa wajen fuskantar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasarmu da kuma yin kafaɗa da kafaɗa da takwarorinsu na duniya wajen gudanar da ayyukan shige da fice.

“A wannan gaɓa, ina taya murna ga kwamandan NITSA da ma’aikatansa bisa kafa tarihi a yau, gaskiyar magana ita ce, aiki ne na farkon wanda ya horar da waɗannan zaƙaƙuran jami’ai, da farko sun kasance kamar ba za su iya ba, lallai ka gudanar da gagarumin aiki wanda ka cancanci yabo, hukumar gudanarwa ta NIS tana alfahari da kai bisa jajircewa wajen gudanar da aiki.” In ji CGI Jere.

Ana sa rai waɗannan jami’ai mata su taimaka wa ƙarfafa tsaron iyakokin da za a tura su kamar yadda NIS ta ƙudurta bisa jagorancin

Tsaro
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.