Wasu manoma guda bakwai sun mutu nan take, bayan da tsawa ta sauka a kansu yayin da suke samun mafaka a karkashin wata bishiya.
Rahotanni daga Indiya, na cewa tsawa ta kashe mutane bakwai yawancinsu manoma a wani kauye da ke arewacin jihar Uttar Pradesh.
‘Yan sanda sun ce tsautsayin ya ritsa da manoman ne a lokacin da suke samun mafaka daga saukar ruwan sama a karkashin wata bishiya a ranar Talata.
Yanzu haka dai hukumomi jihar sun tabbatar da adadin mutane 49 wadanda tsawa ta yi ajalinsu a cikin mako guda.
Wannan ya sa gwamnatin daukar sabbin matakai na nuna wa mutane dabarun kare kansu daga tsawa.
A baya-bayan ma mamakon ruwan sama a yankin kudancin kasar, ya lalata gidaje da dukiyoyi masjmu tarin yawa.
Lamarin da ya sanya gomman mutane rasa matsuguninsu, wanda hakan ya sa aka shiga tallafa musu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp