• Leadership Hausa
Tuesday, March 21, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

by Sadiq
8 months ago
in Manyan Labarai
0
DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An shiga cikin tashin hankali a wasu sassa na Abeokuta, babban birnin jihar Ogun a ranar Lahadi biyo bayan kama wani da ake zargin shugaban kungiyar Boko Haram ne.

Wani gidan rediyo mai zaman kansa a Abeokuta ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi da yamma wanda ya haifar da firgici a tsakanin mazauna jihar.

  • Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus
  • ISWAP Ce Ta Kai Wa Sojoji Hari A Dutsen Zuma – Rahoto

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar tsaro ta farin kaya sun kama wanda ake zargin ne a daren ranar Asabar.

Labarin ya bazu a shafukan sada zumunta na jihar a ranar Lahadi.

Lamarin dai na da nasaba da shirin kai hare-hare a wasu jihohin Kudu maso Yamma da ake zargin ‘yan ta’adda na shirin yi.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Kwace Kujerar Kakakin Majalisar Dokokin Yobe Da Tazarar Kuri’u 182

Mahara Sun Harbi Ma’aikaciyar INEC A Kuros Riba

Sai dai wata majiya mai tushe ta shaida wa wakilinmu cewa an kama wanda ake zargin shugaban kungiyar Boko Haram ne kwanaki a unguwar Ijaye da ke Abeokuta.

Majiyar ta ce tun da farko wanda ake zargin ya yi turjiya kafin ya mika wuya ta karfin tsiya ga jami’an DSS.

A cewar mai binciken, an gudanar da aikin ne a daren ranar Asabar.

A rahoton da gidan rediyon ya bayar, ya ce dan ta’addan da ake zargin ya isa Abeokuta ne daga Katsina, inda ya yi aikin tsaro a Ijaye, inda ya ke tattara bayanan sirri kan hare-haren ta’addanci.

Majiyar tsaron ta ce, “Shi (wanda ake zargin) ya koma Abeokuta ne domin ya kafa kungiyar ‘yan ta’adda domin yin garkuwa da mutane da kuma kai hare-haren ta’addanci.

“Kuma bayan wani taron sirri da aka yi, jami’an tsaro dauke da bindigogi sun kai farmaki maboyarsa sannan suka damke shi.

“Ba abu ne mai sauki ba. Amma da yardar Allah zamu shawo kan lamarin.

“Har yanzu akwai da yawa daga cikinsu, amma muna kan gabar aikinmu.”

Wakilinmu ya tattaro cewa wanda ake zargin yana hannun DSS har yanzu.

Da aka tuntubi kakakin hukumar DSS, Peter Afunanya, bai amsa sakon da aka aike masa ba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, ya ce bai da masaniya kan lamarin.

Tags: 'Yan ta'addaDan Ta'addaDSSJami'an TsaroKwamandan Boko Haramogun
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus

Next Post

Tsawa Ta Kashe Mutane 47 A Indiya

Related

PDP Ta Kwace Kujerar Kakakin Majalisar Dokokin Yobe Da Tazarar Kuri’u 182
Manyan Labarai

PDP Ta Kwace Kujerar Kakakin Majalisar Dokokin Yobe Da Tazarar Kuri’u 182

2 days ago
Mahara Sun Harbi Ma’aikaciyar INEC A Kuros Riba
Manyan Labarai

Mahara Sun Harbi Ma’aikaciyar INEC A Kuros Riba

2 days ago
An Harbe Tsohon Kansila Har Lahira Kan Zargin Sace Akwatin Zabe A Kano
Manyan Labarai

An Harbe Tsohon Kansila Har Lahira Kan Zargin Sace Akwatin Zabe A Kano

2 days ago
Makomata Na Hannun Allah, In Ji Gawuna Dan Takarar APC A Kano
Manyan Labarai

Makomata Na Hannun Allah, In Ji Gawuna Dan Takarar APC A Kano

3 days ago
‘Yansanda Sun Cafke Wakilan PDP 2 Suna Sayen Kuri’a A Ogun
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Cafke Wakilan PDP 2 Suna Sayen Kuri’a A Ogun

3 days ago
Ya Kamata Jami’an Tsaro Su Sake Dagewa  —Abba Gida-Gida
Manyan Labarai

Ya Kamata Jami’an Tsaro Su Sake Dagewa  —Abba Gida-Gida

3 days ago
Next Post
Tsawa Ta Kashe Mutane 47 A Indiya

Tsawa Ta Kashe Mutane 47 A Indiya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da Rahoto Game Da Halin Dimokuradiyya A Amurka A Shekarar 2022

Sin Ta Fitar Da Rahoto Game Da Halin Dimokuradiyya A Amurka A Shekarar 2022

March 21, 2023
Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

March 21, 2023
An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

March 20, 2023
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

March 20, 2023
Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

March 20, 2023
Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

March 20, 2023
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

An Sace Baturen Zabe Akan Hanyarsa Ta Zuwa Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe A Zamfara

March 20, 2023
Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

March 20, 2023
Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

March 20, 2023
An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

March 20, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.