ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

by Sadiq
4 years ago
Boko Haram

An shiga cikin tashin hankali a wasu sassa na Abeokuta, babban birnin jihar Ogun a ranar Lahadi biyo bayan kama wani da ake zargin shugaban kungiyar Boko Haram ne.

Wani gidan rediyo mai zaman kansa a Abeokuta ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi da yamma wanda ya haifar da firgici a tsakanin mazauna jihar.

  • Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus
  • ISWAP Ce Ta Kai Wa Sojoji Hari A Dutsen Zuma – Rahoto

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar tsaro ta farin kaya sun kama wanda ake zargin ne a daren ranar Asabar.

ADVERTISEMENT

Labarin ya bazu a shafukan sada zumunta na jihar a ranar Lahadi.

Lamarin dai na da nasaba da shirin kai hare-hare a wasu jihohin Kudu maso Yamma da ake zargin ‘yan ta’adda na shirin yi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Sai dai wata majiya mai tushe ta shaida wa wakilinmu cewa an kama wanda ake zargin shugaban kungiyar Boko Haram ne kwanaki a unguwar Ijaye da ke Abeokuta.

Majiyar ta ce tun da farko wanda ake zargin ya yi turjiya kafin ya mika wuya ta karfin tsiya ga jami’an DSS.

A cewar mai binciken, an gudanar da aikin ne a daren ranar Asabar.

A rahoton da gidan rediyon ya bayar, ya ce dan ta’addan da ake zargin ya isa Abeokuta ne daga Katsina, inda ya yi aikin tsaro a Ijaye, inda ya ke tattara bayanan sirri kan hare-haren ta’addanci.

Majiyar tsaron ta ce, “Shi (wanda ake zargin) ya koma Abeokuta ne domin ya kafa kungiyar ‘yan ta’adda domin yin garkuwa da mutane da kuma kai hare-haren ta’addanci.

“Kuma bayan wani taron sirri da aka yi, jami’an tsaro dauke da bindigogi sun kai farmaki maboyarsa sannan suka damke shi.

“Ba abu ne mai sauki ba. Amma da yardar Allah zamu shawo kan lamarin.

“Har yanzu akwai da yawa daga cikinsu, amma muna kan gabar aikinmu.”

Wakilinmu ya tattaro cewa wanda ake zargin yana hannun DSS har yanzu.

Da aka tuntubi kakakin hukumar DSS, Peter Afunanya, bai amsa sakon da aka aike masa ba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, ya ce bai da masaniya kan lamarin.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Tsawa Ta Kashe Mutane 47 A Indiya

Tsawa Ta Kashe Mutane 47 A Indiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.