• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana kiwon tantabaru namiji da mace ne, sannan suna kasancewa a tare har zuwa iya tsawon rayuwarsu, suna kuma shafe shekaru daga 12 zuwa 15 suna rayuwa, inda namjin ne ke samo cifci, don gina musu gida.

Haka zalika, a kullum suke yin kwai kuma suna kai wa kimanin shekaru biyar suna yi, kazalika ana yi musu baye; macen da namijin, kana suna daukar daga kimanin kwana 17 zuwa 18 suna kyankyasar kwai.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas
  • FCTA Ta Rushe Gidaje Dubu 15 Da Aka Gina Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Unguwar Gwarinpa Da Ke Abuja

Har ila yau, cikin ‘ya’yan tattabarun da aka kyankyashe na dauke da abincin da za su rika ci har zuwa kwana hudu, inda macen ke ciyar da ‘ya’yan daga kwana goma  har zuwa lokacin da ‘ya’yan za su fara cin abinci da kansu, bayan kwana 26.

Matakan Fara Kiwon Tantabaru

Kiwon tantabara, sananne ne a Nijeriya; musamman a Arewacin wannan kasa ganin cewa, yara kanana su ma na da sha’awar yin wannan kiwo.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Har ila yau, tabbabara na nuna alamu na son zaman lafiya, inda hakan ya sa ake tashin su a wasu bukuwa na wanzar da zaman lafiya a fadin duniya.

Haka zalika, da dan karamin jari za ka iya shiga wannan harka, duk da cewa; an fi saurin samun riba idan aka rungumi fannin ta hanyar amfani da kayan kiwo na zamani; sabanin na gargajiya.

Mahimmancin Kiwon Su:

Daga watanni biyar zuwa shida; sun fara yin kwai, sannan kuma ba su da wata wahalar sarrafawa wajen kiwo, don haka za iya kiwata su har a bayan daki, idan kuma suka kai kimanin kwana 18, sai su fara kyankyasar kwai.

Daga sati uku zuwa hudu, za ka iya cin naman ‘ya’yan; haka nan idan ka zuba jari kadan, za ka samu riba mai yawa.

Wannan kiwo, ya kasance yana samar da kudaden shiga masu yawa ga wadanda suka rungumi wannan fanni a kasashe kamar Bangaladash, Indiya, Nijeriya, Pakistan da sauransu.

Wajen Kwanansu:

Ya na da kyau ka sama musu gurin kwana mai kyau tare da gina musu daki mai tsawo, don ba su kariya daga kai harin musamman muzuru, kare da sauran dabbobi masu illa, haka nan, a kuma tabbatar da dakin na samun shigar wadatacciyar Iska tare da sanya fitila.

Har wa yau, za ka iya gina dakin da katako ko ka yi na kwali, domin kuwa kowace tattabara na bukatar sararin da ya kai kimanin tsawon mita 30 da kuma fadin mita 30 a waje. Haka na, yana da kyau a rika tsaftace dakinsu, akalla sau biyu a wata ko a kullum, sannan ana so abincinsu da ruwan shansu, ya kasance a kusa da dakinsu.

Ciyar Dasu Abinci:

Bugu da kari, tattabaru sun fi cin  Alkama, Masara, Shinkafa da sauran dangoginsu, ana kuma so mai kiwon su ya tabbatar ya ajiye musu abincinsu a kusa da dakinsu na kwana, ana kuma so abincin nasu ya kasance mai gina jiki, musamman don idan sun ci su girma da wuri tare da samun koshin lafiya.

Haka nan, ana so mai kiwon nasu ya tabbatar da tukunyar ruwansu ta na sha na kusa da dakinsu na kwana tare da kula da tsaftarsa.

Lokacin Fara Kwansu:

Macen tantabara na fara yin kwai, bayan ta kai wata biyar zuwa shida, sannan kuma tana yin kwan ne duk bayan wata guda, macen da namijin ne ke kyankyashe kwan daya bayan daya, har ila yau, suna kai wa kwana daga sha bakwai zuwa sha takwas suna wannan kyankyasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabarun Noman  Kankana A Nijeriya

Next Post

Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

11 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

18 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.