• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana kiwon tantabaru namiji da mace ne, sannan suna kasancewa a tare har zuwa iya tsawon rayuwarsu, suna kuma shafe shekaru daga 12 zuwa 15 suna rayuwa, inda namjin ne ke samo cifci, don gina musu gida.

Haka zalika, a kullum suke yin kwai kuma suna kai wa kimanin shekaru biyar suna yi, kazalika ana yi musu baye; macen da namijin, kana suna daukar daga kimanin kwana 17 zuwa 18 suna kyankyasar kwai.

  • Da ÆŠumi-É—umi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas
  • FCTA Ta Rushe Gidaje Dubu 15 Da Aka Gina Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Unguwar Gwarinpa Da Ke Abuja

Har ila yau, cikin ‘ya’yan tattabarun da aka kyankyashe na dauke da abincin da za su rika ci har zuwa kwana hudu, inda macen ke ciyar da ‘ya’yan daga kwana goma  har zuwa lokacin da ‘ya’yan za su fara cin abinci da kansu, bayan kwana 26.

Matakan Fara Kiwon Tantabaru

Kiwon tantabara, sananne ne a Nijeriya; musamman a Arewacin wannan kasa ganin cewa, yara kanana su ma na da sha’awar yin wannan kiwo.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Har ila yau, tabbabara na nuna alamu na son zaman lafiya, inda hakan ya sa ake tashin su a wasu bukuwa na wanzar da zaman lafiya a fadin duniya.

Haka zalika, da dan karamin jari za ka iya shiga wannan harka, duk da cewa; an fi saurin samun riba idan aka rungumi fannin ta hanyar amfani da kayan kiwo na zamani; sabanin na gargajiya.

Mahimmancin Kiwon Su:

Daga watanni biyar zuwa shida; sun fara yin kwai, sannan kuma ba su da wata wahalar sarrafawa wajen kiwo, don haka za iya kiwata su har a bayan daki, idan kuma suka kai kimanin kwana 18, sai su fara kyankyasar kwai.

Daga sati uku zuwa hudu, za ka iya cin naman ‘ya’yan; haka nan idan ka zuba jari kadan, za ka samu riba mai yawa.

Wannan kiwo, ya kasance yana samar da kudaden shiga masu yawa ga wadanda suka rungumi wannan fanni a kasashe kamar Bangaladash, Indiya, Nijeriya, Pakistan da sauransu.

Wajen Kwanansu:

Ya na da kyau ka sama musu gurin kwana mai kyau tare da gina musu daki mai tsawo, don ba su kariya daga kai harin musamman muzuru, kare da sauran dabbobi masu illa, haka nan, a kuma tabbatar da dakin na samun shigar wadatacciyar Iska tare da sanya fitila.

Har wa yau, za ka iya gina dakin da katako ko ka yi na kwali, domin kuwa kowace tattabara na bukatar sararin da ya kai kimanin tsawon mita 30 da kuma fadin mita 30 a waje. Haka na, yana da kyau a rika tsaftace dakinsu, akalla sau biyu a wata ko a kullum, sannan ana so abincinsu da ruwan shansu, ya kasance a kusa da dakinsu.

Ciyar Dasu Abinci:

Bugu da kari, tattabaru sun fi cin  Alkama, Masara, Shinkafa da sauran dangoginsu, ana kuma so mai kiwon su ya tabbatar ya ajiye musu abincinsu a kusa da dakinsu na kwana, ana kuma so abincin nasu ya kasance mai gina jiki, musamman don idan sun ci su girma da wuri tare da samun koshin lafiya.

Haka nan, ana so mai kiwon nasu ya tabbatar da tukunyar ruwansu ta na sha na kusa da dakinsu na kwana tare da kula da tsaftarsa.

Lokacin Fara Kwansu:

Macen tantabara na fara yin kwai, bayan ta kai wata biyar zuwa shida, sannan kuma tana yin kwan ne duk bayan wata guda, macen da namijin ne ke kyankyashe kwan daya bayan daya, har ila yau, suna kai wa kwana daga sha bakwai zuwa sha takwas suna wannan kyankyasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabarun Noman  Kankana A Nijeriya

Next Post

Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

1 day ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

1 day ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.