ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya

by Abubakar Abba
2 years ago
Tattabaru

Ana kiwon tantabaru namiji da mace ne, sannan suna kasancewa a tare har zuwa iya tsawon rayuwarsu, suna kuma shafe shekaru daga 12 zuwa 15 suna rayuwa, inda namjin ne ke samo cifci, don gina musu gida.

Haka zalika, a kullum suke yin kwai kuma suna kai wa kimanin shekaru biyar suna yi, kazalika ana yi musu baye; macen da namijin, kana suna daukar daga kimanin kwana 17 zuwa 18 suna kyankyasar kwai.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas
  • FCTA Ta Rushe Gidaje Dubu 15 Da Aka Gina Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Unguwar Gwarinpa Da Ke Abuja

Har ila yau, cikin ‘ya’yan tattabarun da aka kyankyashe na dauke da abincin da za su rika ci har zuwa kwana hudu, inda macen ke ciyar da ‘ya’yan daga kwana goma  har zuwa lokacin da ‘ya’yan za su fara cin abinci da kansu, bayan kwana 26.

ADVERTISEMENT

Matakan Fara Kiwon Tantabaru

Kiwon tantabara, sananne ne a Nijeriya; musamman a Arewacin wannan kasa ganin cewa, yara kanana su ma na da sha’awar yin wannan kiwo.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Har ila yau, tabbabara na nuna alamu na son zaman lafiya, inda hakan ya sa ake tashin su a wasu bukuwa na wanzar da zaman lafiya a fadin duniya.

Haka zalika, da dan karamin jari za ka iya shiga wannan harka, duk da cewa; an fi saurin samun riba idan aka rungumi fannin ta hanyar amfani da kayan kiwo na zamani; sabanin na gargajiya.

Mahimmancin Kiwon Su:

Daga watanni biyar zuwa shida; sun fara yin kwai, sannan kuma ba su da wata wahalar sarrafawa wajen kiwo, don haka za iya kiwata su har a bayan daki, idan kuma suka kai kimanin kwana 18, sai su fara kyankyasar kwai.

Daga sati uku zuwa hudu, za ka iya cin naman ‘ya’yan; haka nan idan ka zuba jari kadan, za ka samu riba mai yawa.

Wannan kiwo, ya kasance yana samar da kudaden shiga masu yawa ga wadanda suka rungumi wannan fanni a kasashe kamar Bangaladash, Indiya, Nijeriya, Pakistan da sauransu.

Wajen Kwanansu:

Ya na da kyau ka sama musu gurin kwana mai kyau tare da gina musu daki mai tsawo, don ba su kariya daga kai harin musamman muzuru, kare da sauran dabbobi masu illa, haka nan, a kuma tabbatar da dakin na samun shigar wadatacciyar Iska tare da sanya fitila.

Har wa yau, za ka iya gina dakin da katako ko ka yi na kwali, domin kuwa kowace tattabara na bukatar sararin da ya kai kimanin tsawon mita 30 da kuma fadin mita 30 a waje. Haka na, yana da kyau a rika tsaftace dakinsu, akalla sau biyu a wata ko a kullum, sannan ana so abincinsu da ruwan shansu, ya kasance a kusa da dakinsu.

Ciyar Dasu Abinci:

Bugu da kari, tattabaru sun fi cin  Alkama, Masara, Shinkafa da sauran dangoginsu, ana kuma so mai kiwon su ya tabbatar ya ajiye musu abincinsu a kusa da dakinsu na kwana, ana kuma so abincin nasu ya kasance mai gina jiki, musamman don idan sun ci su girma da wuri tare da samun koshin lafiya.

Haka nan, ana so mai kiwon nasu ya tabbatar da tukunyar ruwansu ta na sha na kusa da dakinsu na kwana tare da kula da tsaftarsa.

Lokacin Fara Kwansu:

Macen tantabara na fara yin kwai, bayan ta kai wata biyar zuwa shida, sannan kuma tana yin kwan ne duk bayan wata guda, macen da namijin ne ke kyankyashe kwan daya bayan daya, har ila yau, suna kai wa kwana daga sha bakwai zuwa sha takwas suna wannan kyankyasa.

Tattabaru
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.