ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya

by Abubakar Abba
3 years ago
Tattabaru

Ana kiwon tantabaru namiji da mace ne, sannan suna kasancewa a tare har zuwa iya tsawon rayuwarsu, suna kuma shafe shekaru daga 12 zuwa 15 suna rayuwa, inda namjin ne ke samo cifci, don gina musu gida.

Haka zalika, a kullum suke yin kwai kuma suna kai wa kimanin shekaru biyar suna yi, kazalika ana yi musu baye; macen da namijin, kana suna daukar daga kimanin kwana 17 zuwa 18 suna kyankyasar kwai.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas
  • FCTA Ta Rushe Gidaje Dubu 15 Da Aka Gina Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Unguwar Gwarinpa Da Ke Abuja

Har ila yau, cikin ‘ya’yan tattabarun da aka kyankyashe na dauke da abincin da za su rika ci har zuwa kwana hudu, inda macen ke ciyar da ‘ya’yan daga kwana goma  har zuwa lokacin da ‘ya’yan za su fara cin abinci da kansu, bayan kwana 26.

ADVERTISEMENT

Matakan Fara Kiwon Tantabaru

Kiwon tantabara, sananne ne a Nijeriya; musamman a Arewacin wannan kasa ganin cewa, yara kanana su ma na da sha’awar yin wannan kiwo.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Har ila yau, tabbabara na nuna alamu na son zaman lafiya, inda hakan ya sa ake tashin su a wasu bukuwa na wanzar da zaman lafiya a fadin duniya.

Haka zalika, da dan karamin jari za ka iya shiga wannan harka, duk da cewa; an fi saurin samun riba idan aka rungumi fannin ta hanyar amfani da kayan kiwo na zamani; sabanin na gargajiya.

Mahimmancin Kiwon Su:

Daga watanni biyar zuwa shida; sun fara yin kwai, sannan kuma ba su da wata wahalar sarrafawa wajen kiwo, don haka za iya kiwata su har a bayan daki, idan kuma suka kai kimanin kwana 18, sai su fara kyankyasar kwai.

Daga sati uku zuwa hudu, za ka iya cin naman ‘ya’yan; haka nan idan ka zuba jari kadan, za ka samu riba mai yawa.

Wannan kiwo, ya kasance yana samar da kudaden shiga masu yawa ga wadanda suka rungumi wannan fanni a kasashe kamar Bangaladash, Indiya, Nijeriya, Pakistan da sauransu.

Wajen Kwanansu:

Ya na da kyau ka sama musu gurin kwana mai kyau tare da gina musu daki mai tsawo, don ba su kariya daga kai harin musamman muzuru, kare da sauran dabbobi masu illa, haka nan, a kuma tabbatar da dakin na samun shigar wadatacciyar Iska tare da sanya fitila.

Har wa yau, za ka iya gina dakin da katako ko ka yi na kwali, domin kuwa kowace tattabara na bukatar sararin da ya kai kimanin tsawon mita 30 da kuma fadin mita 30 a waje. Haka na, yana da kyau a rika tsaftace dakinsu, akalla sau biyu a wata ko a kullum, sannan ana so abincinsu da ruwan shansu, ya kasance a kusa da dakinsu.

Ciyar Dasu Abinci:

Bugu da kari, tattabaru sun fi cin  Alkama, Masara, Shinkafa da sauran dangoginsu, ana kuma so mai kiwon su ya tabbatar ya ajiye musu abincinsu a kusa da dakinsu na kwana, ana kuma so abincin nasu ya kasance mai gina jiki, musamman don idan sun ci su girma da wuri tare da samun koshin lafiya.

Haka nan, ana so mai kiwon nasu ya tabbatar da tukunyar ruwansu ta na sha na kusa da dakinsu na kwana tare da kula da tsaftarsa.

Lokacin Fara Kwansu:

Macen tantabara na fara yin kwai, bayan ta kai wata biyar zuwa shida, sannan kuma tana yin kwan ne duk bayan wata guda, macen da namijin ne ke kyankyashe kwan daya bayan daya, har ila yau, suna kai wa kwana daga sha bakwai zuwa sha takwas suna wannan kyankyasa.

Tattabaru
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.