• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

by Muhammad
10 months ago
in Masarautu, Adabi, Al'adu
0
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)

Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar Tsofaffin Ɗalibai na Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da haɗin guiwar Tsofaffin ɗaliban Sashen Nazarin Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero Kano ajin shekara ta 2015 ta miƙa sakon godiya ga Masarautar Hausawan Turai da ke birnin Paris na ƙasar Faransa da Mai Martaba Sarkin Hausawan Turai, Alhaji Sirajou Djankaɗo, bisa naɗi ɗan wannan ƙungiya kuma shugabanta, Alhaji Hassan Baita Ubawaru a matsayin Ma’ajin Hausawan Turai a ranar Lahadi 14 ga Yulin 2024.

Muhammad Bashir Aminu lokacin da yake miƙa wa Ma'ajin Hausawan Turai kyauta a madadin Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami'ar Bayero aji na 2015.
Ma’ajin Hausawan Turai, Alh. Hassan Baita Ubawaru, yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu

Sakataren ƙungiyar, Muhammad Bashir Amin ne ya aike da wannan saƙon a madadin kungiyar ga Masarautar Hausawan Turai da Mai Martaba Alh. Sirajou Djankaɗo a wajen taron walimar taya murna da karramawa da abokan Mai girma Ma’ajin Hausawan Turai suka shirya masa a birnin Kano a ranar Litinin 29 ga Yulin 2024.

  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

A jawabin na Muhammad Bashir, ya ce tabbas an ajiye ƙwarya a gurbinta bisa zaɓo mutum mai nagarta da amana da hidimtawa a al’umma irin Alh. Hassan Baita Ubawaru, a wannan matsayi kuma uwa uba daman shi Hassan ɗin masani ne a fannin ilimin harshe da adabi da al’adun Hausawa don kuwa ya samu shaidar digirinsa na farko a harshen Hausa.

Ma'ajin Hausawan Turai yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu
Ma’ajin Hausawan Turai yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu

“Haƙiƙa an karrama mu kuma mun ji daɗin wannan karamcin ƙwarai da gaske, kuma ƙungiya za ta ci gaba da ganin wannan karamcin har abada, za kuma mu kyautata alaƙa mai kyau da wannan Masarauta ta Hausawan Turai ta fuskar bunƙasa harshe da adabi da al’adun Hausawa da taimakon mabuƙata ” cewar Muhammad Bashir.

Sakataren ƙungiyar a ƙarshe ya aike da sakonsa na taya murna a madadin mambobin kungiyar ga sabon Ma’ajin Hausawan Turai, Alh. Hassan Baita Ubawaru, bisa naɗa shi a wannan matsayi na sarauta mai girma da Allah ya sa ya zama mutum na farko a tarihi da aka naɗa a Masarautar Hausawan Turai.

Labarai Masu Nasaba

GORON JUMA’A 16/05/2025

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Bashir ya yi fatan Ma’ajin Turai ya ninka ayyukansa na alheri da ya saba da kuma yin haƙuri da hidimar jama’a da taimakon mabuƙata, ya kuma yi addu’ar Allah ya kama masa, ya taya shi riƙon kafa tarihi na alheri a wannan Masarauta mai girma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alh. Hassan Baita UbawaruBUKFaransaJami'ar Bayero KanoMa'ajin Hausawan TuraiMasarautar Hausawan TuraiParis
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kakkarfan Tsarin Tsaro Na Zamani A Kan Iyakoki Da Teku Da Sama

Next Post

Zanga-zanga: Shugaban Majalisa Ya Roki ‘Yan Nijeriya Su Kara Ba Wa Tinubu Lokaci 

Related

GORON JUMA’A 16/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 16/05/2025

20 hours ago
Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

4 weeks ago
GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 28-03-2025

2 months ago
GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 14-02-2025

3 months ago
Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

4 months ago
GORON JUMA’A 12-12-2024
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 9-01-2025

4 months ago
Next Post
Zanga-zanga: Shugaban Majalisa Ya Roki ‘Yan Nijeriya Su Kara Ba Wa Tinubu Lokaci 

Zanga-zanga: Shugaban Majalisa Ya Roki 'Yan Nijeriya Su Kara Ba Wa Tinubu Lokaci 

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

May 17, 2025
Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

May 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

May 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

May 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.