Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo, ya musanta jita-jitar ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
A wata sanarwa daga mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Umar Sani, Sambo ya ce labarin ba gaskiya ba ne, kuma an ƙirƙire shi ne don ruɗar da jama’a.
- Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
- Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka
Ya bayyana cewa hoton da ake yaɗawa wanda ya nuna shi tare da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, tsohon hoto ne.
Ya ce sn ɗauki hoton ne shekaru da suka wuce lokacin da gwamnan ya kai masa ziyara a Abuja don jajanta masa bisa rasuwar ɗan uwansa, marigayi Sani Sambo.
Umar Sani, ya bayyana cewa Sambo har yanzu yana cikin jam’iyyar PDP, kuma ba shi da niyyar komawa wata jam’iyya.
Wasu na ganin jita-jitar ta samo asali ne bayan wani abokin aikinsa na baya, Sani Sidi, ya koma jam’iyyar APC tare da magoya bayansa a Kaduna.
Amma Sambo ya ce hakan bai shafe shi ba.
Hakazalika, an shirya Sambo zai halarci bikin ƙaddamar da asibiti mai gadaje 300 da ke Kaduna a ranar Alhamis, 19 ga watan Yuni, 2025.
Ya halarci bikin kuma hakan ba yana nufin ya goyi bayan wata jam’iyya ba ne.
Ƙungiyarsa ta nanata cewa Sambo yana nan daram a cikin jam’iyyar PDP, kuma labarin sauya sheƙar nasa ƙarya ce da aka ƙirƙira domin tayar da hankali da ƙoƙarin cimma wasu muradu na siyasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp