ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

by Sadiq
12 months ago
Buhari

Tsohon mai bai wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, shawara kan harkokin yaɗa labarai, Femi Adesina, ya janyo ce-ce-ku-ce bayan da ya ce da Buhari ya dogara da asibitocin Nijeriya, da ya daɗe da rasuwa.

Adesina ya faɗi haka ne a wani shiri na musamman a gidan talabijin na Channels da aka gabatar domin tunawa da Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti da ke Landan a ranar Lahadi.

  • HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Wasu sun soki yadda Buhari ke yawan zuwa ƙasashen waje domin neman lafiya.

ADVERTISEMENT

Amma Adesina ya kare shi, inda ya bayyana cewa Buhari ya daɗe yana zuwa asibiti a Landan tun kafin ya zama shugaban ƙasa a 2015.

“Likitocin can sun san rashin lafiyarsa sosai,” in ji Adesina.

LABARAI MASU NASABA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

“Ba saboda wasa yake zuwa can ba, ya yarda da su, kuma sun san yadda za su kula da shi.”

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin asibitocin Nijeriya ba su da kayan aiki da ƙwararrun ma’aikata da za su iya kula da lafiyar Buhari.

“In da ya dogara da wasu asibitocinmu, wataƙila da tuni ya riga mu gidan gaskiya,” in ji shi.

Wannan furuci ya ƙara jawo muhawara a faɗin ƙasar game da halin da harkar kiwon lafiya na Nijeriya ke ciki, da kuma yadda manyan ‘yan siyasa ke fita ƙetare don neman magani.

Buhari, ya shugabanci Nijeriya daga shekarar 2015 zuwa 2023.

A lokacin mulkinsa, musamman a shekarun farko, ya sha zuwa ƙasar Birtaniya domin neman lafiya, amma ba a taɓa bayyana cutar da ke damunsa ba.

Ya rasu ne a wani asibiti da ke Landan a ƙarshen mako, kuma mutuwarsa ta haifar da muhawara a faɗin ƙasar.

Za a gudanar da jana’izarsa a ranar Talata a Daura, a Jihar Katsina.

MASU ALAKA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

LABARAI MASU NASABA

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.