ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

by Sadiq
11 months ago
Buhari

Tsohon mai bai wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, shawara kan harkokin yaɗa labarai, Femi Adesina, ya janyo ce-ce-ku-ce bayan da ya ce da Buhari ya dogara da asibitocin Nijeriya, da ya daɗe da rasuwa.

Adesina ya faɗi haka ne a wani shiri na musamman a gidan talabijin na Channels da aka gabatar domin tunawa da Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti da ke Landan a ranar Lahadi.

  • HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Wasu sun soki yadda Buhari ke yawan zuwa ƙasashen waje domin neman lafiya.

ADVERTISEMENT

Amma Adesina ya kare shi, inda ya bayyana cewa Buhari ya daɗe yana zuwa asibiti a Landan tun kafin ya zama shugaban ƙasa a 2015.

“Likitocin can sun san rashin lafiyarsa sosai,” in ji Adesina.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

“Ba saboda wasa yake zuwa can ba, ya yarda da su, kuma sun san yadda za su kula da shi.”

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin asibitocin Nijeriya ba su da kayan aiki da ƙwararrun ma’aikata da za su iya kula da lafiyar Buhari.

“In da ya dogara da wasu asibitocinmu, wataƙila da tuni ya riga mu gidan gaskiya,” in ji shi.

Wannan furuci ya ƙara jawo muhawara a faɗin ƙasar game da halin da harkar kiwon lafiya na Nijeriya ke ciki, da kuma yadda manyan ‘yan siyasa ke fita ƙetare don neman magani.

Buhari, ya shugabanci Nijeriya daga shekarar 2015 zuwa 2023.

A lokacin mulkinsa, musamman a shekarun farko, ya sha zuwa ƙasar Birtaniya domin neman lafiya, amma ba a taɓa bayyana cutar da ke damunsa ba.

Ya rasu ne a wani asibiti da ke Landan a ƙarshen mako, kuma mutuwarsa ta haifar da muhawara a faɗin ƙasar.

Za a gudanar da jana’izarsa a ranar Talata a Daura, a Jihar Katsina.

MASU ALAKA

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni
Manyan Labarai

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.