• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

UEFA Ta Wanke Barcelona Daga Zargin Kashe Kudi Ba Bisa Ka’ida Ba

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
UEFA

Hukumar kula da wasan kwallon kafa ta Turai (Uefa ) ta wanke Barcelona na wucin-gadi domin buga gasar cin kofin zakarun Turai ta 2023 zuwa 2024 a wani bincike da hukumar ta Uefa ke yi kan zargin da aka yi wa kungiyar na biyan kudade ga shugaban alkalan wasa.

A watan Maris ne UEFA ta tabbatar da cewa tana duba yiwuwar biyan kudaden da Barcelona ta biya domin samun goyon bayan alkalan wasa sai dai tun a lokacin Barcelona ta musanta aikata laifin.

  • Kasar Sin Na Goyon Bayan Shimfida Zaman Lafiya A Colombia
  • Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

Yayin da aka bai wa Barcelona izinin shiga gasar zakarun Turai, UEFA tana ikon hukunta kungiyar a nan gaba amma daman binciken na Uefa ya zo ne bayan da ofishin mai shigar da kara na Barcelona ya gabatar da wani binciken laifuka a ranar 10 ga Maris. An yi zargin cewa Barcelona ta biya Yuro miliyan 8.4 ga tsohon mataimakin shugaban kwamitin alkalan wasa na Spain da kamfaninsa na Dasnil 95, wato Jose Maria Enrikuez Negreira.

An tuhumi Barca da tsoffin jami’an kungiyar da Negreira da laifin almundahana da cin amana da kuma gabatar da takardar kasuwanci ta karya kuma bayanin kudaden, wanda gidan rediyon Ser Catalunya ya bayyana a watan Fabrairu, ya fito fili ne bayan wani bincike da hukumomin haraji

suka yi kan kamfanin Dasnil 95, mallakan Negreira.

LABARAI MASU NASABA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Barcelona ta amince cewa kungiyar ta biya Dasnil 95, don tattara rahotannin bidiyo da suka shafi kwararrun alkalan wasa da nufin inganta bayanan da masu horon ‘yan wasa ke bukata

Kungiyar ta kara da cewa yin kwangilar rahotannin al’ada ce a tsakanin manyan kungiyoyin kwallon kafa a duniya sai dai yanzu ana jira aga nan gaba wanne irin mataki hukumar zata dauka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya
Wasanni

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba
Wasanni

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa
Wasanni

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Ake Noma Tan  Miliyan 12.4 Kacal Na Masara A Wasu Sassan Nijeriya -Shugaba

Dalilin Da Ya Sa Ake Noma Tan  Miliyan 12.4 Kacal Na Masara A Wasu Sassan Nijeriya -Shugaba

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.