ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Ake Noma Tan  Miliyan 12.4 Kacal Na Masara A Wasu Sassan Nijeriya -Shugaba

by Abubakar Abba
3 years ago
Masara

Shugaban kungiyar manoman masara na kasa Dakta Bello Abubakar Funtua ya bayyana cewa, Masara tan miliyan 12.4 kacal aka iya noma wa kasar, sakamakon matsalolin ambaliyar a wasu sassa na kudu maso-gabas da kuma arewa maso gabas na kasar nan.

Bello ya sanar da hakan ne a wani taron kwararru a fannin na noman Masara da aka gudanar a kwanan baya, inda ya kara da cewa, kazalika  karancin taki a wasu sassa na yankankunan,  ya kara janyo rashin nomanta kamar yadda ake bukata.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6
  • Gwamnatin Jihar Gombe Na Bai Wa Fannin Noman Auduga  Mahimmanci – Kwamishina

“Tan miliyan 12.4 na Masara kacal aka iya noma wa a sakamakon matsalolin ambaliyar ruwa da karancin taki a wasu sassa na yankankunan kudu maso-gabas da kuma arewa ta gabas da arewa ta yamma.”

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa, a yanzu Nijeriya na samar da Masara ninki goma ne kawai, inda ya kara da cewa, daga 1999 zuwa shekara ta 2019, a duk shekara masarar da ake nomawa a Nijeriya ta na ninkawa sau biyu.

A cewarsa, hakan ya sanya daga 2014 zuwa 2019 Nijeriya ta zama kasa ta biyu kan noman Masara a Afrika, inda take noma Masara tan miliyan 10.8 a duk shekara baya ga Afrika ta Kudu wadda take kan gaba a noman Masara a nahiyar Afrika, da take noma masara tan miliyan 12.9 a duk shekara.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Bello, ya yi bayyana cewa shekara ta 2014 Nijeriya ta noma Masara tan miliyan 10.1 inda a 2015 ta noma tan miliyan 11.6, sai a 2016 da ta noma tan miliyan 11.6, sai shekarar 2017 ta noma tan miliyan 10.4, a 2018 zuwa 2019 ta noma kimanin tan miliyan 11.0.

” Daga 2014 zuwa 2019 Nijeriya ta zama kasa ta biyu kan noman Masara a Afrika, inda take noma Masara tan miliyan 10.8 a duk shekara baya ga Afrika ta Kudu wadda take kan gaba a noman Masara a nahiyar Afrika, da take noma masara tan miliyan 12.9 a duk shekara.”

Bello ya kuma buga misali da cewa, a shekaru biyar na tsohowar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Nijeriya tana noma masara tan miliyan 10.8 a duk shekara.

Ya bayyana cewa, Masarar da Nijeriya ta noma a shekara ta 2019 tan miliyan 12.6 ta yi kasa idan aka yi la’akari da wadda ta noma a shekarar 2020 a sakamakon matsalar karancin ruwan sama,

“Masarar da Nijeriya ta noma a shekara ta 2019 tan miliyan 12.6 ta yi kasa idan aka yi la’akari da wadda ta noma a shekarar 2020 a sakamakon matsalar karancin ruwan sama. ”

A na sa jawabin Darakta Janar na Majalisar samar da iri ta kasa Dakta  Philip Ojo, ya nanata mahimmancin akan shuka ingantacce Irin Masara, musamman domin manomanta su samu riba mai yawa.

Ya ce, ya zuwa yanzu an samar da irin shuka na masara daban-daban har 140, don ganin an bunkasa  noman Masara  a Nijeriya .

” Akwai matukar mahimmancin akan shuka ingantacce Irin Masara, musamman domin manomanta su samu riba mai yawa. ”

Shi kuwa wani kwararre a fannin  Mista Joseph Kibaki ya bayyana cewa, akwai bukatar a samar da kyawawan tsare -tsare da shirye shirye, musamman daga bangaren gwamnatin tarayya domin a kara bunkasa fannin noman Masara a daukacin fadin kasar nan.

“Akwai  bukatar a samar da kyawawan tsare -tsare da shirye shirye, musamman daga bangaren gwamnatin tarayya domin a kara bunkasa fannin noman Masara a daukacin fadin kasar nan.”

Su kuwa wasu masana a fannin noman Masara a kasar nan sun bayyana wasu hanyoyin da ya dace a dauka domin a kara bunkasa noman Masara a kasar nan.

Sun sanar da hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki a fannin suka gudanar tare da kuma kokarin lalubo da mafita kan kalubalen da fannin ke fuskanta.

Mahalarta taron sun kuma attaunawa kan kalubale da fannin ke fuskanta a kasar nan tare da kuma bayar da shawarwari, musamman ga gwamnatin tarayya kan yadda a lalubo da mafita akan kalubalen.

Masara
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Kasar Sweden Ta Yi Waje Rod Da Kasar Amurka A Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon Mata

Kasar Sweden Ta Yi Waje Rod Da Kasar Amurka A Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon Mata

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.