• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Shahada

Tura dai ta fara kai al’umma bango dangane da irin cin kashin da ‘yan bindiga masu garguwa da mutane ke yi, inda wata uwa mai suna Maryam Muhammad ‘yar shekara 52 ta ceci rayuwar danta daga hannun masu garkuwa a kauyen Sabon Garin Jada da ke karamar hukumar Alkaleri a Jihar Bauchi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Malama Maryam ta gamu da ajalinta a lokacin da ta kare danta daga hannun masu garkuwa da mutane, inda ta yi kukan kura ta nufi kansu da tabarya har ma ta karya daya daga cikin masu garkuwan, lamarin da ya sanya suka bude mata wuta har ta rasu nan take.

  • Da Diminsa: ‘Yan Daba Sun Farmaki ‘Yan Majalisar Bauchi Tare Da Farfasa Motoci

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, Marigayiya Maryam mai ‘ya’ya takwas a duniya ta nufi kan masu garkuwa da mutanen ne a lokacin da suka mamaye gidanta da ke sabon Garin Jada da nufin su yi garkuwa da danta ko illata shi, inda ta ce sam hakan ba zai yiyu ba.

Idan za ku iya tunawa dai, a ranar Alhamis da ta gabata ne dai wasu gungun ‘yan bindiga suka kashe mutum hudu tare da mutum uku a wani harin da suka kai yankin Alkaleri.

Wakilinmu ya zanta da diyar marigayiyar, Hauwa’u Muhammad ‘yar shekara 26, inda ta yi cikakken bayanin yadda lamari ya faru, ta ce, ‘yan bindigan sun so sace yayanta ne sai kuma mamarsu ta yi kokarin hana su har sai da ‘yan bindigan suka bude mata wuta.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

“Da daren ranar Litinin da misalin karfe 12 wasu mutane suka shigo cikin gidanmu tare da kokarin yin garkuwa da yayana. Ita kuma mahaifiyarmu ta taso domin ta taimaka masa, a wannan yanayin ne suka harbe har lahira, inda muke addu’a Allah ya mata rahama,” Hauwau ta shaida cikin kuka.

Ta kara da cewa yayan nata bai mutu ba, amma sun ji masa raunuka a kai. Ta ce ‘yan bindigan da suka shigo gidansu sun kai mutum 11.

Da yake nasa jawabin a wajen jajantawa kan rasuwar marigayiya a ranar Asabar da gabata, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad Abdulkadir ya ayyana Marigayiya Maryam a matsayin wata jarumar da ta bar abin koyi ga al’umma, ya misalta cewa lokacin da za a ji tsoron ‘yan bindiga ya wuce.

A cewarsa, “Abun da ya faru a wannan garin a gaskiya ya zama abun jaje sosai a garemu. Mun rasa ‘yar uwa, muna fatan Allah ya amshi shahadarta.

Wannan mata ta zama abin koyi a garemu a matsayinta na uwa wacce ta nuna mana mata ma suna iya jajircewa, ba ta yi mutuwar banza ba, ta yi mutuwar shahada insha Allahu, Allah ya jikanta ya rahama.”

Gwamna Bala Muhammad ya daura da cewa, “Mun zo nan garin ne domin mu jajanta muku ga wannan lamari wanda ya zama ruwan dare a Nijeriya.

“A yadda ake ma Jihar Bauchi tana da tsaro, amma abun yana son ya addabemu, sai dai ba za mu kwanta muna barci ba, za mu yi iya bakin kokarinmu mu wajen rayukanku da dukiyarku, kuma ya kamata a sani tsaro abu ne da ya kasance hakki ne a kan kowa.”

Gwamnan ya roki sarakuna da malamai da jama’a da su kara ninka addu’o’i domin samun nasarar shawo kan matsalolin tsaro da suke addabar kasar nan. Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da suke amsa kiran jama’a a kowani tare da hanzarin kawo dauki idan jama’a sun bukaci hakan, musamman a lokacin da suke cikin yanayi na neman agajin gaggawa.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Alkaleri, Yusuf Garba ya bayyana cewar suna samun matsalar tsaro a yankinsu ne sakamakon iyaka da suka yi da jihohin Bauchi da Taraba wanda aka kashe mutum hudu a garin, ya nemi hadin kan jama’a domin samun nasara.

Shi kuma kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Umar Sanda ya roki jama’a ne da su samar musu da bayanan sirri da zai taimaka wa hukumomin tsaro a kowani lokaci wajen yaki da matsalar tsaro.

A ‘yan kwanakin baya dai an yi ta samu rahotonnin matsalolin tsaro a Jihar Bauchi don ko a kwanakin baya ma an yi garkuwa da Hakimin kauyen Zira da ke karamar hukumar Toro tare da dansa daga bisani aka sako su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version