• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Tallafawa Mata 500 Da Buhunan Gyada Da Tsabar Kudi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Tallafawa Mata 500 Da Buhunan Gyada Da Tsabar Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan gwamnan jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta baiwa mata 500 manyan buhunan gyada da tallafin kudi a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi.

Uwargida, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce karamar hukumar Arewa ita ce ta fara cin gajiyar shirin da za a gudanar a daukacin kananan hukumomi 21 na jihar don taimaka wa mata wajen kasuwancinsu don dogaro da kai.

  • Ambaliyar Ruwan Sama Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 3 A Jihar Kebbi
  • Ambaliya: NEMA Ta Bada Tallafin Kayayyakin Agaji Ga Mutane 22,202 A Kebbi

Ta bayyana hakan ne a lokacin da take raba kayan tallafi da kudade ga mata 500 da suka ci gajiyar tallafi a karamar hukumar Arewa ta jihar, wanda ya gudana a harabar karamar hukumar.

A wajen rabon tallafin, kowacce daga cikin mata 500 da suka ci gajiyar tallafin ta samu manyan buhunan gyada guda biyu na biredin gyada, don yin (Kuli-Kuli) da tsabar kudi Naira dubu goma (N 10,000). Ta kuma bayyana cewa, babban dalilin da ya sa aka ba su wannan tallafin shi ne don baiwa wadanda suka ci gajiyar tallafin damar tura ’ya’yansu a makarantun Boko da na addini a garuruwansu, inda ta jaddada cewa ilimi ba shi da wata tangarda, ginshikin rayuwa da ci gaban al’umma ne.

Sai dai kuma ta yi kira ga sarakunan gargajiya a jihar da su ba gwamnati goyon baya da hadin kan da ake bukata domin bunkasa fannin ilimi da inganci da sabbin abubuwa.

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

“Samar da ci gaban ilimi zai zama abin al’ajabi ba tare da sa hannun sarakunan gargajiya musamman hakimai”, inji ta.

Dan Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, a Mazabar Arewa, Hon. Nura Kangiwa ya godewa uwargidan gwamnan bisa wannan karimcin, inda ya ba da tabbacin cewa majalisar za ta ba gwamnatin gwamna Nasir Idris hadin kan da ya dace domin cimma burinta na ci gaba.

Mai-Arewa Kangiwa, Alhaji Yusuf Sulieman ya baiwa uwargidan gwamna Sarautar gargajiya na “Madugar Arewa, Shugabar Matar Arewa”, a lokacin da ta ziyarce shi a fadarsa.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Hafsat Yusuf ta nuna godiyarta ga uwargidan gwamnan bisa ba su tallafin kudi da buhunan gyada. Ta kara da cewa hakan zai kara habaka kasuwancinsu na Kuli-Kulin gyada a cikin Al’ummarsu. Haka Kuma ta tabbatar wa matar gwamnan cewa “za mu yi amfani da tallafin ta hanyar da ya dace”, inji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiTallafiUwargidan Gwamnan Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Nasarori Sama Da 1100 A Gun CIFTIS Na Shekarar 2023

Next Post

Firaministan Kasar Sin Ya Bukaci Japan Da Ta Bi Hanyar Da Ta Dace Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliya

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

4 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

5 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

7 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

8 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

9 hours ago
Next Post
Japan

Firaministan Kasar Sin Ya Bukaci Japan Da Ta Bi Hanyar Da Ta Dace Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.