• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Tallafawa Mata 500 Da Buhunan Gyada Da Tsabar Kudi

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

Uwargidan gwamnan jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta baiwa mata 500 manyan buhunan gyada da tallafin kudi a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi.

Uwargida, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce karamar hukumar Arewa ita ce ta fara cin gajiyar shirin da za a gudanar a daukacin kananan hukumomi 21 na jihar don taimaka wa mata wajen kasuwancinsu don dogaro da kai.

  • Ambaliyar Ruwan Sama Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 3 A Jihar Kebbi
  • Ambaliya: NEMA Ta Bada Tallafin Kayayyakin Agaji Ga Mutane 22,202 A Kebbi

Ta bayyana hakan ne a lokacin da take raba kayan tallafi da kudade ga mata 500 da suka ci gajiyar tallafi a karamar hukumar Arewa ta jihar, wanda ya gudana a harabar karamar hukumar.

A wajen rabon tallafin, kowacce daga cikin mata 500 da suka ci gajiyar tallafin ta samu manyan buhunan gyada guda biyu na biredin gyada, don yin (Kuli-Kuli) da tsabar kudi Naira dubu goma (N 10,000). Ta kuma bayyana cewa, babban dalilin da ya sa aka ba su wannan tallafin shi ne don baiwa wadanda suka ci gajiyar tallafin damar tura ’ya’yansu a makarantun Boko da na addini a garuruwansu, inda ta jaddada cewa ilimi ba shi da wata tangarda, ginshikin rayuwa da ci gaban al’umma ne.

Sai dai kuma ta yi kira ga sarakunan gargajiya a jihar da su ba gwamnati goyon baya da hadin kan da ake bukata domin bunkasa fannin ilimi da inganci da sabbin abubuwa.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

“Samar da ci gaban ilimi zai zama abin al’ajabi ba tare da sa hannun sarakunan gargajiya musamman hakimai”, inji ta.

Dan Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, a Mazabar Arewa, Hon. Nura Kangiwa ya godewa uwargidan gwamnan bisa wannan karimcin, inda ya ba da tabbacin cewa majalisar za ta ba gwamnatin gwamna Nasir Idris hadin kan da ya dace domin cimma burinta na ci gaba.

Mai-Arewa Kangiwa, Alhaji Yusuf Sulieman ya baiwa uwargidan gwamna Sarautar gargajiya na “Madugar Arewa, Shugabar Matar Arewa”, a lokacin da ta ziyarce shi a fadarsa.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Hafsat Yusuf ta nuna godiyarta ga uwargidan gwamnan bisa ba su tallafin kudi da buhunan gyada. Ta kara da cewa hakan zai kara habaka kasuwancinsu na Kuli-Kulin gyada a cikin Al’ummarsu. Haka Kuma ta tabbatar wa matar gwamnan cewa “za mu yi amfani da tallafin ta hanyar da ya dace”, inji ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Labarai

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Kebbi
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Next Post
Japan

Firaministan Kasar Sin Ya Bukaci Japan Da Ta Bi Hanyar Da Ta Dace Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Kebbi

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.