• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Tallafawa Mata 500 Da Buhunan Gyada Da Tsabar Kudi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Tallafawa Mata 500 Da Buhunan Gyada Da Tsabar Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan gwamnan jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta baiwa mata 500 manyan buhunan gyada da tallafin kudi a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi.

Uwargida, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce karamar hukumar Arewa ita ce ta fara cin gajiyar shirin da za a gudanar a daukacin kananan hukumomi 21 na jihar don taimaka wa mata wajen kasuwancinsu don dogaro da kai.

  • Ambaliyar Ruwan Sama Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 3 A Jihar Kebbi
  • Ambaliya: NEMA Ta Bada Tallafin Kayayyakin Agaji Ga Mutane 22,202 A Kebbi

Ta bayyana hakan ne a lokacin da take raba kayan tallafi da kudade ga mata 500 da suka ci gajiyar tallafi a karamar hukumar Arewa ta jihar, wanda ya gudana a harabar karamar hukumar.

A wajen rabon tallafin, kowacce daga cikin mata 500 da suka ci gajiyar tallafin ta samu manyan buhunan gyada guda biyu na biredin gyada, don yin (Kuli-Kuli) da tsabar kudi Naira dubu goma (N 10,000). Ta kuma bayyana cewa, babban dalilin da ya sa aka ba su wannan tallafin shi ne don baiwa wadanda suka ci gajiyar tallafin damar tura ’ya’yansu a makarantun Boko da na addini a garuruwansu, inda ta jaddada cewa ilimi ba shi da wata tangarda, ginshikin rayuwa da ci gaban al’umma ne.

Sai dai kuma ta yi kira ga sarakunan gargajiya a jihar da su ba gwamnati goyon baya da hadin kan da ake bukata domin bunkasa fannin ilimi da inganci da sabbin abubuwa.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

“Samar da ci gaban ilimi zai zama abin al’ajabi ba tare da sa hannun sarakunan gargajiya musamman hakimai”, inji ta.

Dan Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, a Mazabar Arewa, Hon. Nura Kangiwa ya godewa uwargidan gwamnan bisa wannan karimcin, inda ya ba da tabbacin cewa majalisar za ta ba gwamnatin gwamna Nasir Idris hadin kan da ya dace domin cimma burinta na ci gaba.

Mai-Arewa Kangiwa, Alhaji Yusuf Sulieman ya baiwa uwargidan gwamna Sarautar gargajiya na “Madugar Arewa, Shugabar Matar Arewa”, a lokacin da ta ziyarce shi a fadarsa.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Hafsat Yusuf ta nuna godiyarta ga uwargidan gwamnan bisa ba su tallafin kudi da buhunan gyada. Ta kara da cewa hakan zai kara habaka kasuwancinsu na Kuli-Kulin gyada a cikin Al’ummarsu. Haka Kuma ta tabbatar wa matar gwamnan cewa “za mu yi amfani da tallafin ta hanyar da ya dace”, inji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiTallafiUwargidan Gwamnan Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Nasarori Sama Da 1100 A Gun CIFTIS Na Shekarar 2023

Next Post

Firaministan Kasar Sin Ya Bukaci Japan Da Ta Bi Hanyar Da Ta Dace Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliya

Related

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

2 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

3 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

4 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

5 hours ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

13 hours ago
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Labarai

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

14 hours ago
Next Post
Japan

Firaministan Kasar Sin Ya Bukaci Japan Da Ta Bi Hanyar Da Ta Dace Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.