• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Tallafawa Mata 500 Da Buhunan Gyada Da Tsabar Kudi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Tallafawa Mata 500 Da Buhunan Gyada Da Tsabar Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan gwamnan jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta baiwa mata 500 manyan buhunan gyada da tallafin kudi a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi.

Uwargida, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce karamar hukumar Arewa ita ce ta fara cin gajiyar shirin da za a gudanar a daukacin kananan hukumomi 21 na jihar don taimaka wa mata wajen kasuwancinsu don dogaro da kai.

  • Ambaliyar Ruwan Sama Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 3 A Jihar Kebbi
  • Ambaliya: NEMA Ta Bada Tallafin Kayayyakin Agaji Ga Mutane 22,202 A Kebbi

Ta bayyana hakan ne a lokacin da take raba kayan tallafi da kudade ga mata 500 da suka ci gajiyar tallafi a karamar hukumar Arewa ta jihar, wanda ya gudana a harabar karamar hukumar.

A wajen rabon tallafin, kowacce daga cikin mata 500 da suka ci gajiyar tallafin ta samu manyan buhunan gyada guda biyu na biredin gyada, don yin (Kuli-Kuli) da tsabar kudi Naira dubu goma (N 10,000). Ta kuma bayyana cewa, babban dalilin da ya sa aka ba su wannan tallafin shi ne don baiwa wadanda suka ci gajiyar tallafin damar tura ’ya’yansu a makarantun Boko da na addini a garuruwansu, inda ta jaddada cewa ilimi ba shi da wata tangarda, ginshikin rayuwa da ci gaban al’umma ne.

Sai dai kuma ta yi kira ga sarakunan gargajiya a jihar da su ba gwamnati goyon baya da hadin kan da ake bukata domin bunkasa fannin ilimi da inganci da sabbin abubuwa.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

“Samar da ci gaban ilimi zai zama abin al’ajabi ba tare da sa hannun sarakunan gargajiya musamman hakimai”, inji ta.

Dan Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, a Mazabar Arewa, Hon. Nura Kangiwa ya godewa uwargidan gwamnan bisa wannan karimcin, inda ya ba da tabbacin cewa majalisar za ta ba gwamnatin gwamna Nasir Idris hadin kan da ya dace domin cimma burinta na ci gaba.

Mai-Arewa Kangiwa, Alhaji Yusuf Sulieman ya baiwa uwargidan gwamna Sarautar gargajiya na “Madugar Arewa, Shugabar Matar Arewa”, a lokacin da ta ziyarce shi a fadarsa.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Hafsat Yusuf ta nuna godiyarta ga uwargidan gwamnan bisa ba su tallafin kudi da buhunan gyada. Ta kara da cewa hakan zai kara habaka kasuwancinsu na Kuli-Kulin gyada a cikin Al’ummarsu. Haka Kuma ta tabbatar wa matar gwamnan cewa “za mu yi amfani da tallafin ta hanyar da ya dace”, inji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiTallafiUwargidan Gwamnan Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Nasarori Sama Da 1100 A Gun CIFTIS Na Shekarar 2023

Next Post

Firaministan Kasar Sin Ya Bukaci Japan Da Ta Bi Hanyar Da Ta Dace Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliya

Related

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

2 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

13 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

14 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

16 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

16 hours ago
Next Post
Japan

Firaministan Kasar Sin Ya Bukaci Japan Da Ta Bi Hanyar Da Ta Dace Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.