• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Varane Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallon Kafa Yanada Shekara 31

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
1 year ago
Varane

Tsohon dan wasan bayan Real Madrid da Manchester United kuma dan kasar Faransa, Raphael Varane, ya yi ritaya daga buga kwallon kafa yanada shekara 31.

 

Varane ya koma kungiyar kwallon kafa ta Como dake kasar Italiya a kyauta a watan Yuli amma ya ji rauni a gwiwarsa a wasansa na farko da Sampdoria a watan jiya.

  • Muna Fatan Sterling Ya Bai Wa Mara Ɗa Kunya A Arsenal – Arteta
  • An Gudanar Da Taro Mai Taken “A Rubuce A Sama: Labarina Na Kasar Sin” Don Murnar Cika Shekaru 75 Da Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin a Mexico da Australiya

Duk da haka, dan wasan bayan ya ce zai ci gaba da zama a kungiyar domin ya taimaka wa kungiyar a wasu hanyoyin da ba na shiga filin wasa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Varane ya fara taka leda a kungiyar Lens ta Faransa inda ya shafe kakar wasa daya a kungiyar kafin ya koma Real Madrid a shekarar 2011.

 

Ya taka rawar gani na tsawon shekaru 10 a babban birnin Madrid na kasar Spain, inda ya lashe kofuna 18 – ciki har da kofunan La Liga uku da na gasar zakarun Turai hudu.

 

Mai tsaron bayan ya koma Old Trafford a lokacin bazara na shekarar 2021 kan fam miliyan 34, inda ya buga wasanni 95 a duk gasannin da ya bugawa Manchester United.

 

Ya lashe kofin Carabao a shekarar 2022 kuma wasansa na karshe a kungiyar shi ne nasarar cin kofin FA na karshe akan abokan hamayyar Man Utd wato Manchester City a Wembley a watan Mayu.

 

A bangaren wasannin kasa da kasa Varane ya buga wasansa na farko ga kasar Faransa a shekara ta 2013 inda ya buga mata wasanni 93 jimilla,sannan ya lashe gasar cin kofin duniya a shekarar 2018, da gasar Nations League a shekarar 2021 kuma ya sake kai wasan karshe na gasar cin kofin duniya a shekarar 2022.

 

“Ba ni da nadama, ba zan canza komai ba, na yi nasara fiye da burin da nake dashi,ina kuma alfahari da cewa na yi kokarin barin ko’ina fiye da yadda na same shi inji Varane a wani rubutu da yayi a shafinsa na sada zumunta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
Wasanni

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
Next Post
Amurka

Yarjejeniyar Samoa: Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Hukuncin NMCC Kan Zargin Auren Jinsi

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.