• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Varane Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallon Kafa Yanada Shekara 31

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
1 year ago
Varane

Tsohon dan wasan bayan Real Madrid da Manchester United kuma dan kasar Faransa, Raphael Varane, ya yi ritaya daga buga kwallon kafa yanada shekara 31.

 

Varane ya koma kungiyar kwallon kafa ta Como dake kasar Italiya a kyauta a watan Yuli amma ya ji rauni a gwiwarsa a wasansa na farko da Sampdoria a watan jiya.

  • Muna Fatan Sterling Ya Bai Wa Mara Ɗa Kunya A Arsenal – Arteta
  • An Gudanar Da Taro Mai Taken “A Rubuce A Sama: Labarina Na Kasar Sin” Don Murnar Cika Shekaru 75 Da Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin a Mexico da Australiya

Duk da haka, dan wasan bayan ya ce zai ci gaba da zama a kungiyar domin ya taimaka wa kungiyar a wasu hanyoyin da ba na shiga filin wasa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Varane ya fara taka leda a kungiyar Lens ta Faransa inda ya shafe kakar wasa daya a kungiyar kafin ya koma Real Madrid a shekarar 2011.

 

Ya taka rawar gani na tsawon shekaru 10 a babban birnin Madrid na kasar Spain, inda ya lashe kofuna 18 – ciki har da kofunan La Liga uku da na gasar zakarun Turai hudu.

 

Mai tsaron bayan ya koma Old Trafford a lokacin bazara na shekarar 2021 kan fam miliyan 34, inda ya buga wasanni 95 a duk gasannin da ya bugawa Manchester United.

 

Ya lashe kofin Carabao a shekarar 2022 kuma wasansa na karshe a kungiyar shi ne nasarar cin kofin FA na karshe akan abokan hamayyar Man Utd wato Manchester City a Wembley a watan Mayu.

 

A bangaren wasannin kasa da kasa Varane ya buga wasansa na farko ga kasar Faransa a shekara ta 2013 inda ya buga mata wasanni 93 jimilla,sannan ya lashe gasar cin kofin duniya a shekarar 2018, da gasar Nations League a shekarar 2021 kuma ya sake kai wasan karshe na gasar cin kofin duniya a shekarar 2022.

 

“Ba ni da nadama, ba zan canza komai ba, na yi nasara fiye da burin da nake dashi,ina kuma alfahari da cewa na yi kokarin barin ko’ina fiye da yadda na same shi inji Varane a wani rubutu da yayi a shafinsa na sada zumunta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana
Wasanni

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
Wasanni

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Next Post
Amurka

Yarjejeniyar Samoa: Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Hukuncin NMCC Kan Zargin Auren Jinsi

LABARAI MASU NASABA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

October 23, 2025
Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.