• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

by El-Zaharadeen Umar
10 months ago
in Kasashen Ketare
0
Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da taron hadin kan ‘yan jarida na kasashen Afirka masu amfani da harshen Hausa a Niamey da ke kasar Nijar.

wannan taro dai, shi ne na farko da aka taba yi domin cimma wani buri da yake da alaka da masu harkaR yada labarai da kuma kasashen Afrika masu amfani da harshen Hausa da niyyar canza alakar yadda ake tafiyar DA harkokin sadarwa a Nahiyar Afrika.

  • Turkiyya Da Nijar Na Tattauna Ƙulla Kawancen Soji Da Tattalin Arziki
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Tuba A Kasar Nijar

Wata fitacciyar ‘yar jarida da ke aiki da babar tashar talabijin ta kasar Nijar, wato RTN (Tele Sahel), Hajiya Maryam Lawali Sarkin Arzen ta assasa kungiyar da za a gudanar da wannan aikin a karkashinta, wanda kuma take samun goyan hukumomi a kasar ta Nijar.

Babban manufar kafa kungiyar da kuma irin ayyukan da za a yi karkashin wannan tafiya shi ne, canza tunani ko alakar yadda ake yada labarai a kasashen Afrika masu amfani da harsunan gida, inda aka ba harshen Hausa babar dama fiye da kowane yare.

 

Labarai Masu Nasaba

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Taken wannan taron shi ne, “Inganta zaman lafiya da hadin kai da kwanciyar hankali ta hanyar harshen Hausa da tabbatar da ‘yancin kai na kasashen Afrika,” wanda masana daga kasashe daban-daban suka tattauna kan wadannan batutuwa tare da ba ta mafita a kan wannan kudiri.

Taron ya samu halatar wakilai daga kasashe goma sha daya na Afrika da suke amfani da harshen Hausa wajen yada labarai, kimanin baki 2,500 aka gayyato da ‘yan jaridu 100 daga kasashe 11 da suka hada Nijeriya da Sudan da Chadi da Barki-Nafaso da Mali da Nijar da Benin da Kamaru da Togo da sauran kasashen Afrika masu amfani da harshen Hausa.

Shugaban Kasar Nijar, Janar Abdulrahamn Tiani ne ya bude taron na kwana uku da aka yi a baban dakin taron na Mahatma Gandi da ke cikin Birnin Niamey na kasar Nijar.

Janar Tiani wanda ya samu wakilicin Firaminista kuma Ministan Kudi da Tattalin Arziki na Kasar Nijar, Ali Lamine Zeine ya ce shugaban kasa yana tare da wannan taro dari bisa dari saboda muhimmancinsa da kuma kyawawan manufarsa.

Ya kara da cewa, hatta jawabin shugaban kasa an rubuta shi ne da harshen Faransa, amma saboda mahimmcin taron da kuma kungiyar dole aka umarci firaministan ya gabatar da jawabi da Hausa.

Ya ce gwamnatin ceton al’umma karkashin jagorancin Janar Tiani, tana tare da wannan tafiya kuma kofa a bude take domin ba da gudunmawa tare da fatan za a tattauna muhiamman abubuwan da za su amfani kasashen Afrika masu amfani da harshen Hausa domin samun nasara.

NijarNijar

“Ina kira da babar murya ga ‘yan jarida su yi amfani da ilimi da basirar da Allah ya ba su wajen fadakar da al’umma halin da kasa take ciki, kuma su fadi gaskiya kan duk abin da suka gani wanda ba daidai ba, idan kuma an yi na daidai shi ma su fada” in ji shi.

Firaministan ya ce duk abin da mutun ya aikata gobe kiyama sai an tambaye shi kuma sai ya yi bayani, saboda haka dole a fadi gaskiya a wannan aiki da ya shafi rayuwar al’umma da ci gaban kasa da kuma al’umma.

Sannan ya yi tambihin irin matsalolin da aka samu bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar ta Nijar, inda ya ce an samu matsala da rashin fahimta tsakanin kasar tasu da kuma kungiyar habaka tattalin arzikin yammacin Afirka (ECOWAS), wanda har ta kai ga kasar Nijar ta janye daga wannan kungiya.

 

Hamza Almustapha ya nuna muhimmancin amfani da Hausa

Majo Hamza Al-Mustapha na daga cikin manyan bakin da aka gayyata domin halartar wannan taro, kuma ya yi jawabi game da muhimmancin yin amfani da harshen Hausa wajen tafiyar da al’amurran al’umma.

Ya kara da cewa ko lokacin zuwan Turawa sun iske al’umma suna da hankilinsu, suna tunaninsu suna da akidarsu, suna da alkalansu, suna da hukunci, suna da dokokinsu, suna karatu da rubutu, saboda haka babu wani abu da za a nuna wa wannan al’umma.

Al-mustapha ya ce idan wannan al’umma na san ta kwaci kanta daga hannu wadannan ‘yan mulkin mallaka, dole sai an canza yadda suka gurbata abubuwan da suka iska al’umma da su na asali masu kyau.

Haka kuma ya ja hankalin ‘yan jarida musamman wadanda suke amfani da harshen Hausa, inda ya ce suna da muhimmiyar rawa da za su taka wajen canza akalar yadda abubuwa suka tafiya a halin yanzu.

Ya ce ka da ‘yan jaridu su ba da kofa da za a yi amfani da su wajen canza gaskiya zuwa karya, ya ce hakki ne babba kan ‘yan jaridu su fadi abu yadda yake, saboda haka su yi duk mai yiyuwa wajen ganin an samu nasarar wannan taro da kungiya da manufofin da aka tsara ta domin su.

Ya kara da cewa, al’ummar Nijar sun yi abin da ya kamata, saboda haka su kara jajircewa wajen bai wa shugabanin gwamnatin ceton al’umma ta sojoji karkashin jagorancin Janar Abdurahman Tiani domin a samu nasarar da ake bukata.

 

An dauko hanyar tabbatar wa al’umma da ‘yanci – Hajiya Naja’atu

Daya daga cikin ‘yan gwagwarmaya, kuma jigo a siyasar Nijeriya, Hajiya Na’ajatu Mohammad na daga cikin wadanda aka gayyata domin yin jawabi a wajen wannan taro.

Da take nata jawabin, Hajiya Naja’atu ta yaba da wannan taro wanda ta ce an dauki hanyar raba al’umma da bauta, da suka dade suna yi wanda Turawa makiyan Afrika suka kawo.

Ta kara da cewa daga ranar da aka dauke wa al’umma tunani da harshen da ba na su ba, to an bautar da su. Ta ce akwai mamaki ga mutum bakar fata mai kima da daraja, amma sai a ji yana cewa shi Bature ne wanda haka ba daidai ba ne.

“Yanzu yaki ya kare, yanci ba na rago bane, mutanen Nijar ba raggaye ba ne, sannan tsakanin Nijar da kuma Nijeriya a lokacin Daular Usmaniyya abu daya ne, saboda haka duk wanda ya ce yana san raba jini da tsoka, to ranmu yake nema, dole muma mu nemi nashi” in ji ta

Hajiya Naja’atu ta ci gaba da cewa duk wata gwamnati a duniya ana yin ta saboda amfanin ‘yan kasa, idan sojoji za su samar wa da ‘yan kasa abubuwan da suke bukata, Allah ya dawwamar da sojoji a kan mulki.

Kazalika, yar gwagwarmayar ta yi bayanin cewa arzikin da Allah ya yi wa Nahiyar Afrika ya sa Turawan mulkin mallaka suka hana wannan yanki sakat, tana mai cewa dole ne ‘yan Afrika su ci gajiyar arzikin da Allah ya yi masu.

Tattaunawar da aka yi da masana

Bayan kammala wannan taro, an shiga rana ta biyu da ta uku domin tattaunawa da masana kan makomar abubuwan da aka sa gaba karkashin kungiyar hadin kan ‘yan jaridu masu amfani da harshen Hausa a Afrika.

An tsara yadda masana za su gudanar da muhawara kan maudu’i daban-daban da suka shafi aikin jarida a wadannan kasashe kuma baki sun kasance cikin tattaunawar da kuma yin tambayoyi.

Aliyu Rabi’u daga tashar talabijin ta kasa wato NTA na daga cikin mahalarta taro kuma daya daga cikin wadanda za su tattauna da ‘yan jaridu a game da taron.

An ba shi maudu’i mai taken hadin kai a tsakanin ‘yan jaridu, inda ya yi bayanin dangane da abubuwan da suka shafi wannan taro. Bayan kammala jawabinsa aka tabka muhawara bisa kulawar ‘yar jarida daga gidan talabijin da rediyo ta kasa wato RTN.

Bayanan da Aliyu ya yi sun zama wani haske na kudirin da kungiyar ke da shi, na ganin kasashen Afrika masu amfani da harshen Hausa sun maida hankali domin canza alakar yadda suka gudanar da al’amuransu na yau da gobe.

Babu shakka bayanai sun gabata kan muhimmancin hadin kai kan duk wasu al’amurra da suka shafi rayuwar al’umma kai tsaye ba wai a aikin jarida kawai ba.

Shi ma Dakta Salisu na kungiyar kare hakkin Dan’adam, ya yi nasa jawabin ne kan yadda za a samar da ci gaba a tsakanin ‘yan jaridu da gwamnatoci da kungiyar domin cimma wancan manufa da aka samar da kungiyar.

Bayan kammala nasa jawabin an tabka muhawara a tsakanin mahalarta taro, kuma an samu matsaya kan hanyoyin da za a bi domin samun ci gaba a wannan tafiya da kuma abubuwan da za su ta so nan gaba.

Alhaji Tijjani Mustapha Mahadi, ma’akaci a fadar shugaban kasar Chadi, ya yi nasa jawabin ne kan batun da ya dabaibaye harkokin yada labarai wato labarun karya (fake News), inda ya dauki lokaci yana yi wa mahalarta taro bayani da kuma tarihin wannan matsala da hanyoyin maganin ta.

Ya kuma jefa kalubale ga ‘yan jaridu kan rawar da za su taka wajen rage wannan matsala ta labarun karya kafin wata rana ta zama tarihi.

Ya kawo misalai da dama, da irin yadda aka gudanar da aikin jarida a kasar Chadi wanda yana da bambanci a wasu kasashen Afrika musamman masu amfani da harshen Hausa, wanda shi ne ake son a dabaka a wannan kungiya da kuma taron.

An yi muhawara mai tsawo kan yadda jaddawalin tafiyar da wannan kungiya da kuma hanyoyin da za a bi domin tunkarar kalubalen da ‘yan jaridu da kafafen yada labarai suke fuskanta.

A jawabin rufe taro, shugabar kungiyar hadin kai ‘yan jaridu masu amfani da harshen Hausa a Afrika, Hajiya Maryam Lawal Arzein wanda ma’akaciya ce a gidan talabijin na kasa wato RTN, ta yi dogon bayani game da asassa kungiyar.

A cewarta, kafafen yada labarai musamman na Afrika suna fuskantar kalubale da yawa ta hanyar isar da sakon da ya kamata ‘yan kasa su sani.

“Kafa wannan kungiya zai taimaka wajen wayar da kan al’umma su kara sanin hakkin da ya rataya a kan su da kuma hakkin shugabannin kan mabiya, ‘ in ji ta.

Hajiya Maryam ta ce tana da burin ganin an kafa wata gidauniya da za ta rinka tallafa wa ‘yan jaridu musamman wadanda suka ajiye aiki kuma karfinsu ya kare ko mutuwa da makamantansu.

Tana mai cewa, sun gaji da gorin da ake yi wa ‘yan jaridu cewa makwadaita ne masu son abin duniya, inda har ake zargin ana yin amfani da su wajen lalata al’amurra.

Daga karshe ta bayyana cewa za a rika yin irin wannan taro sau biyu a shekara, inda take fatan cewa taro na gaba za a yi shi baban Birnin Tarayya Abuja na Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HausaNijarYan jaridu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

Next Post

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Alhaji Haruna Ɗanyaya Sabon Sarkin Ningi 

Related

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
Kasashen Ketare

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

4 days ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

1 week ago
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
Kasashen Ketare

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

2 weeks ago
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Kasashen Ketare

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

2 weeks ago
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Ketare

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

2 weeks ago
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

2 weeks ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Alhaji Haruna Ɗanyaya Sabon Sarkin Ningi 

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Alhaji Haruna Ɗanyaya Sabon Sarkin Ningi 

LABARAI MASU NASABA

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

July 10, 2025
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

July 10, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

July 10, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato

July 10, 2025
Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista

Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.