• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 month ago
in Ra'ayinmu
0
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne, Nijeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya, domin gudanar da marnar bikin zagowar ranar Yara ta duniya na 2025.

Taken taron na bana shi ne,“ Amfana da Basirar da Yaran suke da ita,”.

  • Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
  • Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Sai dai, wasu Yaran a wasu kasashen duniya, na ci gaba da fusknatar munanan tsagwama iri da ban da ban.

Hatta a Nijeriya, wasu Yaran na ci gaba da fusknatar barazanar ta tsangwama, wanda hakan ke dakushe tananin makomar su, ta gobe.

Irin wannan kalubalen na fuskantar tsagwama da Yara a kasar nan ke fuskanta, abu ne da ya zama waji, a dauki matakin gaggawa, domin magance hakan.

Labarai Masu Nasaba

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

Yawan Yaran da ba su zuwa makarantun boko a Nijeria wadanda suka kai kimanin su miliyan 18.3, hakan ya nuna cewa, wannan adadin na Yaran, kusan daidai yake da yawan alumomin da ke a kasashen Norway, Singapore, da Cuba.

Wannan ba wai batu ne, na matsalar da ake fuskanta a bangaren ilimin boko kadai ba, domin matsala ce, da ke bukatar a ayyana dokar ta baci tare da samar da daukin da ya kamata daga bangaren gwamnati da kuma sauran alomomin kasar.

Misali, wata kungiya mai kare rajin Yara, mai zaman kanta da ake kira da, Sabe the Children ta bayyana cewa, sama da Yara1,600 a shekarar 2014, aka sace a makarantun su, wadanda sace su din, ya zama tamkar, an dana masu wani tarkon mutuwa ne.

Kazalika, wani rahoto Daraktan Asusun tallafawa kannan Yara na UNICEF, da ke gudanar da aikinsa a kasar nan Dakta Tushar Raney a bayyana cewa, a shekarar 2023 kacal, a daukacin fadain Nijeriya, an tilasta garkame makarantu da suka kai adadin 439.

A wani lokacin rashin zabi ne, ke tilastawa wasu iyayen jefa rayuwar ‘ya’yansu, a cikin hatsari domin ‘ya’yan na su, samu ilimin zamani, wanda idan ba su samu ilimin ba, rayuwarsu, za ta kasance a cikin kangin jahilci, duba da cewa, kowanne dan kasa, na da hakkin a bai wa rayuwarsa kariya.

Bugu da kari, kalubalen rashin samun abinci mai gina jiki a tsakanin yaran kasar, na daga cikin abinda ya kara zama wata babbar annoba.

Ganin cewa, a kasar akwai yara kanana miliyan 5.4 da shekarun su suka fara daga watanni 0 zuwa watanni 59 da ke ci gaba da fuskantar kalubalen karancin abinci wadanda adadinsu ya karu zuwa kaso 23 cikin dari, hakan ya sanya, a nan gaba, Nijeriya za ta iya yin rashin samun karin alumma.

Rashin samun abinci mai gina jiki a tsakanin kananan yara hakan ya dashishe su, daga saurin fahintar ilimi tare da jefa rayuwarsu, a cikin kangin talauci da kuma rashin samun ci gaba.

Hakazalika, wasu alkaluman da UNICEF ta fitar sun bayyna cewa, a fadin duniya, an dora Nijeriya kan sikelin kasar da ta kai mataki na uku, wajen yiwa ‘ya’ya mata masu kananna shekaru aure, inda kasar ta kasance, tana da ‘ya’ya mata da suka kai miliyan 23.6 da aka yi masu are, suan da shekaru 18 da kuma wasun su, da suka kai sama da miliyan 10, da aka yi masu aure, su na da shekaru 15.

Irin wannan auren na wuri, ya janyo tauye hakkin irin wadannan ‘ya’yan mata, damar samun ilimin boko, wanda hakan ya kasance, tamkar take masu ‘yancin su ne, na rayuwa.

Hukumar kididdiga ta kasa NBS a cikin wani rahoto da ta fitar ta ce, akwai kuma batun sanya kananna yara aikin bauta, inda a Nijeriya, a 2022 ake kiyasta cewa, akwai yara sama da miliyan 24 da suke yin irin wannan aikin na kangin bauta, ciki har da wasu yara miliyan 14.3 da ake sanya wa, yin ayyuka masu hatsari.

Yaran suna yin aikin ne, a gurare da ban da ban da suka hada da, inda ake hakar ma’adanai da kuma a wasu masana’antu, inda ake biyansu, kudade, ‘yan kalilan.

Sai dai, a kwanukan baya, gwamnatin tarayya ta samar da wani shiri na samar da ilimin boko, inda ta zuba sama da Naira biliyan 263 a asusaun samar da ilimi na bai daya wato UBEC, amma wasu tsaiko da ake samu a shirin, hakan na ci gaba da janyo jinkirin yin aikin gadan-gadan.

Hakazalika, shugaban kasa Bola Tinubu, ya aminci da a yi amfani da asusun na UBEC, musamman domin a bunkasa ilimi a kasar a sama da jihohi 30, amma sai dai, shirin baya tafiya, yadda ya kamata.

Bugu da kari, daukin da ma’aikatar kula da walwalar mata da walwalar a karkashin ministar ma’aikatar Imaan Sulaiman-Ibrahim, ta samar da wani kyakyawan tsari na bai wa kananan yara kariya.

Misali, an karawa ma’aikatar karin kasafin kudi da ya dara sama da kaso 1000 a cikin dari, musamman domin a tabbatar da ana bai wa yaran kasar kariyar da ta kamata.

Sai dai, samar da daukin abu ne, dake bukatar a hada karfi da karfe, a tsakanin matakan gwamnati uku na kasar nan da kuma daukin sauran alumomin kasar.

Abin da Nijeriya ke bukata shi ne, kula da walwala da jin dadin yara tare da kuma samar masu da tsaron rayuwar su.

Kazalika, ya zama wajibi gwamnatin tarayya kafa cibiyoyin ilimi domin a samar da kariyar ta tsaro a shiyoyin kasa, musamman ta hanyar tura jami’an tsaro, domin su bai wa makarantu kariya.

Dole ne kuma gwamnatocin jihohi su tabbatar da sun samar da kudaden a cikin shirin ilimin, wanda hakan zai dakile duk wani jinkiri da ake samu, na wanzar da shirin.

Bugu da kari, ya sama wajibi gwamnati ta samar da kyawawan shirye-shiye na tallafawa iyaye wajen tsamo su, daga halin talaucin da ke addabar su

Ya kamata malaman addinai, su mayar da hankali wajen yin gangamin kan abubuwa da ke sanya wa, ake take wa kananan yara ‘yanci.

Hazalika, akwai bukatar a kara mayar da hankali, wajen kara horas da jami’an tsaro tare da samar masu da wadatattun kudade domin su rinka hukunta duk wanda ya take ‘yancin yara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Next Post

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Related

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
Ra'ayinmu

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

4 weeks ago
Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
Ra'ayinmu

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

1 month ago
Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

3 months ago
NCC
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

4 months ago
Ra'ayinmu

Gangamin Yaki Da Cutar Kuturta A Nijeriya

5 months ago
Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya
Ra'ayinmu

Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya

7 months ago
Next Post
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

July 17, 2025
Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

July 16, 2025
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.