ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

by Leadership Hausa and Sulaiman
5 months ago
Yara

A kwanan baya ne, Nijeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya, domin gudanar da marnar bikin zagowar ranar Yara ta duniya na 2025.

Taken taron na bana shi ne,“ Amfana da Basirar da Yaran suke da ita,”.

  • Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
  • Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Sai dai, wasu Yaran a wasu kasashen duniya, na ci gaba da fusknatar munanan tsagwama iri da ban da ban.

ADVERTISEMENT

Hatta a Nijeriya, wasu Yaran na ci gaba da fusknatar barazanar ta tsangwama, wanda hakan ke dakushe tananin makomar su, ta gobe.

Irin wannan kalubalen na fuskantar tsagwama da Yara a kasar nan ke fuskanta, abu ne da ya zama waji, a dauki matakin gaggawa, domin magance hakan.

LABARAI MASU NASABA

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

Yawan Yaran da ba su zuwa makarantun boko a Nijeria wadanda suka kai kimanin su miliyan 18.3, hakan ya nuna cewa, wannan adadin na Yaran, kusan daidai yake da yawan alumomin da ke a kasashen Norway, Singapore, da Cuba.

Wannan ba wai batu ne, na matsalar da ake fuskanta a bangaren ilimin boko kadai ba, domin matsala ce, da ke bukatar a ayyana dokar ta baci tare da samar da daukin da ya kamata daga bangaren gwamnati da kuma sauran alomomin kasar.

Misali, wata kungiya mai kare rajin Yara, mai zaman kanta da ake kira da, Sabe the Children ta bayyana cewa, sama da Yara1,600 a shekarar 2014, aka sace a makarantun su, wadanda sace su din, ya zama tamkar, an dana masu wani tarkon mutuwa ne.

Kazalika, wani rahoto Daraktan Asusun tallafawa kannan Yara na UNICEF, da ke gudanar da aikinsa a kasar nan Dakta Tushar Raney a bayyana cewa, a shekarar 2023 kacal, a daukacin fadain Nijeriya, an tilasta garkame makarantu da suka kai adadin 439.

A wani lokacin rashin zabi ne, ke tilastawa wasu iyayen jefa rayuwar ‘ya’yansu, a cikin hatsari domin ‘ya’yan na su, samu ilimin zamani, wanda idan ba su samu ilimin ba, rayuwarsu, za ta kasance a cikin kangin jahilci, duba da cewa, kowanne dan kasa, na da hakkin a bai wa rayuwarsa kariya.

Bugu da kari, kalubalen rashin samun abinci mai gina jiki a tsakanin yaran kasar, na daga cikin abinda ya kara zama wata babbar annoba.

Ganin cewa, a kasar akwai yara kanana miliyan 5.4 da shekarun su suka fara daga watanni 0 zuwa watanni 59 da ke ci gaba da fuskantar kalubalen karancin abinci wadanda adadinsu ya karu zuwa kaso 23 cikin dari, hakan ya sanya, a nan gaba, Nijeriya za ta iya yin rashin samun karin alumma.

Rashin samun abinci mai gina jiki a tsakanin kananan yara hakan ya dashishe su, daga saurin fahintar ilimi tare da jefa rayuwarsu, a cikin kangin talauci da kuma rashin samun ci gaba.

Hakazalika, wasu alkaluman da UNICEF ta fitar sun bayyna cewa, a fadin duniya, an dora Nijeriya kan sikelin kasar da ta kai mataki na uku, wajen yiwa ‘ya’ya mata masu kananna shekaru aure, inda kasar ta kasance, tana da ‘ya’ya mata da suka kai miliyan 23.6 da aka yi masu are, suan da shekaru 18 da kuma wasun su, da suka kai sama da miliyan 10, da aka yi masu aure, su na da shekaru 15.

Irin wannan auren na wuri, ya janyo tauye hakkin irin wadannan ‘ya’yan mata, damar samun ilimin boko, wanda hakan ya kasance, tamkar take masu ‘yancin su ne, na rayuwa.

Hukumar kididdiga ta kasa NBS a cikin wani rahoto da ta fitar ta ce, akwai kuma batun sanya kananna yara aikin bauta, inda a Nijeriya, a 2022 ake kiyasta cewa, akwai yara sama da miliyan 24 da suke yin irin wannan aikin na kangin bauta, ciki har da wasu yara miliyan 14.3 da ake sanya wa, yin ayyuka masu hatsari.

Yaran suna yin aikin ne, a gurare da ban da ban da suka hada da, inda ake hakar ma’adanai da kuma a wasu masana’antu, inda ake biyansu, kudade, ‘yan kalilan.

Sai dai, a kwanukan baya, gwamnatin tarayya ta samar da wani shiri na samar da ilimin boko, inda ta zuba sama da Naira biliyan 263 a asusaun samar da ilimi na bai daya wato UBEC, amma wasu tsaiko da ake samu a shirin, hakan na ci gaba da janyo jinkirin yin aikin gadan-gadan.

Hakazalika, shugaban kasa Bola Tinubu, ya aminci da a yi amfani da asusun na UBEC, musamman domin a bunkasa ilimi a kasar a sama da jihohi 30, amma sai dai, shirin baya tafiya, yadda ya kamata.

Bugu da kari, daukin da ma’aikatar kula da walwalar mata da walwalar a karkashin ministar ma’aikatar Imaan Sulaiman-Ibrahim, ta samar da wani kyakyawan tsari na bai wa kananan yara kariya.

Misali, an karawa ma’aikatar karin kasafin kudi da ya dara sama da kaso 1000 a cikin dari, musamman domin a tabbatar da ana bai wa yaran kasar kariyar da ta kamata.

Sai dai, samar da daukin abu ne, dake bukatar a hada karfi da karfe, a tsakanin matakan gwamnati uku na kasar nan da kuma daukin sauran alumomin kasar.

Abin da Nijeriya ke bukata shi ne, kula da walwala da jin dadin yara tare da kuma samar masu da tsaron rayuwar su.

Kazalika, ya zama wajibi gwamnatin tarayya kafa cibiyoyin ilimi domin a samar da kariyar ta tsaro a shiyoyin kasa, musamman ta hanyar tura jami’an tsaro, domin su bai wa makarantu kariya.

Dole ne kuma gwamnatocin jihohi su tabbatar da sun samar da kudaden a cikin shirin ilimin, wanda hakan zai dakile duk wani jinkiri da ake samu, na wanzar da shirin.

Bugu da kari, ya sama wajibi gwamnati ta samar da kyawawan shirye-shiye na tallafawa iyaye wajen tsamo su, daga halin talaucin da ke addabar su

Ya kamata malaman addinai, su mayar da hankali wajen yin gangamin kan abubuwa da ke sanya wa, ake take wa kananan yara ‘yanci.

Hazalika, akwai bukatar a kara mayar da hankali, wajen kara horas da jami’an tsaro tare da samar masu da wadatattun kudade domin su rinka hukunta duk wanda ya take ‘yancin yara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Yara
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Next Post
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

LABARAI MASU NASABA

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.