• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin Na Musamman Ya Karyata Zargin Dake Cewa Wai Kasarsa Na Saka Wa Afirka “Tarkon Bashi”

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Sin Na Musamman Ya Karyata Zargin Dake Cewa Wai Kasarsa Na Saka Wa Afirka “Tarkon Bashi”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wakilin musamman a ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin mai kula da yankin kahon Afirka, Xue Bing, ya karyata kalamai marasa tushe dake cewa, wai kasar Sin tana saka wa Afirka “tarkon bashi”.

Xue, ya bayyana a shekaran jiya Talata a Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha, cewa bai dace a dora wa kasar Sin laifin sanya wa Afirka bashi ba.

  • Shanghai Ta Kara Shigar Da Ridi Daga Afirka

Alkaluman da bankin duniya ya fitar a bara sun nuna cewa, daga cikin bashin dala biliyan 696 da ake bin kasashen Afirka 49, kaso 75 bisa dari bashi ne na cibiyoyin hada-hadar kudi na bangarori daban-daban da ’yan kasuwan dake samar da bashi, abun da ya dauki akasarin bashin da ake bin kasashen Afirka. Kana akwai kaso 35 bisa dari na bashin da cibiyoyin samar da bashi masu zaman kansu na kasashen yammacin duniya ke bin kasashen Afirka, adadin da ya ninka kusan sau uku idan aka kwatanta da bashin da kasashen Afirka suka karba daga kasar Sin.

Domin taimakawa kasashen Afirka rage matsin lambar da suke fuskanta a fannin biyan bashi, kasar Sin ta shiga cikin “shawarar dakatar da biyan bashi” da kasashen G20 suka fitar, da rattaba hannu tare da kasashen Afirka 19 kan yarjejeniyar dakatar da biyan bashi, ko kuma cimma matsaya daya kan ragewa ko soke bashi baki daya. Amma akasin haka, wadanda suka fi sauran bangarori bayar da bashi ga kasashen Afirka, ciki har da masu samar da bashi masu zaman kansu na kasa da kasa, da cibiyoyin hada-hadar kudi na bangarori daban-daban, har yanzu ba su dauki matakan ragewa ko kuma soke bashin da suke bin kasashen Afirka ba.

A dayan bangaren kuma, Xue Bing ya ce, kasar Sin na goyon-bayan kasashen yankin kahon Afirka don su warware bambance-bambancen dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa a wannan yanki.

Labarai Masu Nasaba

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

Bugu da kari, a yayin taron manema labarai da aka shirya yau, wani dan jarida ya yi mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin tambayar cewa: Mene ne ra’ayin kasar Sin game da hadin gwiwa tsakanin kasashe da yankin kahon Afirka?

Wang Wenbin ya ba da amsa cewa, a halin yanzu, Habasha na kan wani muhimmin mataki na dawo da zaman lafiya, da mayar da hankali kan bunkasuwa. Mun yi imanin cewa, ya kamata dukkan kasashe su kara yin ayyukan da za su taimaka wajen ci gaban Habasha da samar da zaman lafiya a yankin baki daya, maimakon kakaba takunkumi don tilastawa ko tsoma baki a harkokin cikin gidan wasu kasashe kan wasu batutuwa masu sarkakiya. Kasar Sin tana son yin aiki tare da ragowar kasashen duniya, don taimakawa yankin na Afirka ya zama ginshikin zaman lafiya da hadin gwiwa da samun bunkasuwa cikin hadin gwiwa.

A dangane da batun kare hakkin bil Adama a kasar Amurka kuwa, Wang Wenbin ya ce, abin da ya dace gwamnatin Amurka ta yi shi ne, ta hanzarta magance matsalolin kare hakkin dan-Adam da ke kara ta’azzara a kasarta, kamar nuna wariyar launin fata, laifuffukan kyama, da matsalar harbin bindiga, da laifukan muggan kwayoyi da dai sauransu. (Mai fassarawa: Murtala Zhang, Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi

Next Post

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Related

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

17 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

18 hours ago
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

19 hours ago
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

2 days ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 days ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

2 days ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

August 11, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.