ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin Na Musamman Ya Karyata Zargin Dake Cewa Wai Kasarsa Na Saka Wa Afirka “Tarkon Bashi”

by CMG Hausa
3 years ago
Afirka

Wakilin musamman a ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin mai kula da yankin kahon Afirka, Xue Bing, ya karyata kalamai marasa tushe dake cewa, wai kasar Sin tana saka wa Afirka “tarkon bashi”.

Xue, ya bayyana a shekaran jiya Talata a Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha, cewa bai dace a dora wa kasar Sin laifin sanya wa Afirka bashi ba.

  • Shanghai Ta Kara Shigar Da Ridi Daga Afirka

Alkaluman da bankin duniya ya fitar a bara sun nuna cewa, daga cikin bashin dala biliyan 696 da ake bin kasashen Afirka 49, kaso 75 bisa dari bashi ne na cibiyoyin hada-hadar kudi na bangarori daban-daban da ’yan kasuwan dake samar da bashi, abun da ya dauki akasarin bashin da ake bin kasashen Afirka. Kana akwai kaso 35 bisa dari na bashin da cibiyoyin samar da bashi masu zaman kansu na kasashen yammacin duniya ke bin kasashen Afirka, adadin da ya ninka kusan sau uku idan aka kwatanta da bashin da kasashen Afirka suka karba daga kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Domin taimakawa kasashen Afirka rage matsin lambar da suke fuskanta a fannin biyan bashi, kasar Sin ta shiga cikin “shawarar dakatar da biyan bashi” da kasashen G20 suka fitar, da rattaba hannu tare da kasashen Afirka 19 kan yarjejeniyar dakatar da biyan bashi, ko kuma cimma matsaya daya kan ragewa ko soke bashi baki daya. Amma akasin haka, wadanda suka fi sauran bangarori bayar da bashi ga kasashen Afirka, ciki har da masu samar da bashi masu zaman kansu na kasa da kasa, da cibiyoyin hada-hadar kudi na bangarori daban-daban, har yanzu ba su dauki matakan ragewa ko kuma soke bashin da suke bin kasashen Afirka ba.

A dayan bangaren kuma, Xue Bing ya ce, kasar Sin na goyon-bayan kasashen yankin kahon Afirka don su warware bambance-bambancen dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa a wannan yanki.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Bugu da kari, a yayin taron manema labarai da aka shirya yau, wani dan jarida ya yi mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin tambayar cewa: Mene ne ra’ayin kasar Sin game da hadin gwiwa tsakanin kasashe da yankin kahon Afirka?

Wang Wenbin ya ba da amsa cewa, a halin yanzu, Habasha na kan wani muhimmin mataki na dawo da zaman lafiya, da mayar da hankali kan bunkasuwa. Mun yi imanin cewa, ya kamata dukkan kasashe su kara yin ayyukan da za su taimaka wajen ci gaban Habasha da samar da zaman lafiya a yankin baki daya, maimakon kakaba takunkumi don tilastawa ko tsoma baki a harkokin cikin gidan wasu kasashe kan wasu batutuwa masu sarkakiya. Kasar Sin tana son yin aiki tare da ragowar kasashen duniya, don taimakawa yankin na Afirka ya zama ginshikin zaman lafiya da hadin gwiwa da samun bunkasuwa cikin hadin gwiwa.

A dangane da batun kare hakkin bil Adama a kasar Amurka kuwa, Wang Wenbin ya ce, abin da ya dace gwamnatin Amurka ta yi shi ne, ta hanzarta magance matsalolin kare hakkin dan-Adam da ke kara ta’azzara a kasarta, kamar nuna wariyar launin fata, laifuffukan kyama, da matsalar harbin bindiga, da laifukan muggan kwayoyi da dai sauransu. (Mai fassarawa: Murtala Zhang, Ibrahim Yaya)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.