• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakiliyar CPPCC Wadda Take Kokarin Neman Mafita Ga Sha’anin Kiwon Reindeer

by CGTN Hausa
2 years ago
CPPCC

Kabilar Ewenki dake zama a yankin Mongoliya ta gida na kasar Sin, an yi mata lakabin “Kabila ta karshe dake yin farauta a kasar Sin”, kuma rayuwar al’ummar kabilar ba ta rabuwa da dabbar Reindeer, dabbar da ta sha bamban da sauran dabobbi, sakamakon yadda Reindeer ke bukatar neman abinci a daji, ba za a iya kiwon su a gida ba. Du Mingyan, ‘yar kabilar Ewenki ce, kuma mamba ce a majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin wato CPPCC a takaice, wadda take kokarin neman mafita wajen kiyaye wannan dabba da taimakawa al’ummar wurin wajen samun arziki dangane da wannan sha’ani.

Sau tari ne malama Du Mingyan ta kai ziyarar bincike a sassan da al’ummar Ewenki ke rayuwa a birnin Hulunbuir dake yankin Mongliya ta gida, don fahimtar yanayin rayuwarsu. Bisa nazarin da take yi, ta gabatar da shawarwari da rahoto har 9 game da yadda za a raya ayyukan kiyaye Reindeer a wurin, kuma karkashin jagorancin hukumar wurin, an kafa yankin kiwon Reindeer na farko na kasar Sin a garin Aoluguya na ‘yan kabilar Ewenki da ke birnin Hulunbuir, an kuma gina wurin shakatawa bisa al’adun ‘yan kabilar Ewenki da ke shafar dabbar Reindeer, wanda ya samu matukar karbuwa daga baki masu yawon shakatawa.

  • Yadda Ake Samosa
  • CPPCC Ya Rufe Cikakken Taronsa Na Shekara-shekara 

An gudanar da taron shekara shekara na CPPCC a kwanan baya a nan birnin Beijing. A matsayinta na ‘yar majalisar CPPCC, Du Mingyan ta gabatar da shawararta, don neman sassan da abin ya shafa su samar da tallafi na manufofi, ta fannin kare dabbobin Reindeer daga cututtuka da kara haiyayyafarsu.

Du Mingyan daya ce daga cikin ‘yan majalisar CPPCC fiye da 2100 da suka fito daga bangarori 34 ciki har da tattalin arziki da al’adu da ba da ilmi da sauransu, wadanda suka hadu a wajen taron majalisar CPPCC don ba da shawarwarinsu game da yadda za a zamanintar da kasar Sin daga fannoni daban daban, don sauke nauyin dake wuyansu na ba da shawara kan harkokin siyasa da sa ido a fannin dimokuradiyya da tsoma baki cikin harkokin kasar.

Majalisar CPPCC na kunshe da wakilai daga jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, da sauran jam’iyyun demokuradiyya da ba na kwaminis ba, da wadanda ba sa cikin kowace jam’iyya, da rukunonin al’umma, da wakilai daga kananan kabilu da bangarori daban-daban, da wakilan ‘yan uwanmu daga Taiwan da Hong Kong da Macao, da wakilan Sinawa mazauna kasashen waje da suka dawo da dai sauran wasu bakin da aka ba su goron gayyata na musamman. (Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Next Post
Ramadan: Sanata Yari Ya Gwangwaje Magidanta 250,000 Da Tallafin Abinci A Zamfara

Ramadan: Sanata Yari Ya Gwangwaje Magidanta 250,000 Da Tallafin Abinci A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.