• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Suka Kai Harin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ne Suka Kai Harin Kuje – Hadimin Gumi

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Wanda Suka Kai Harin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ne Suka Kai Harin Kuje – Hadimin Gumi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hadimin fitaccen Malamin addinin musulunci da ke Jihar Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, Malam Tukur Mamu, ya ce wadanda suka kai hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ne suka kai hari kan gidan yarin Kuje da ke Abuja ne.

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru da ta kai hari tare da yin garkuwa da fasinjoji a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga watan Maris, ta dauki alhakin kai hari gidan yarin Kuje da ke birnin tarayya Abuja, a daren ranar Talata.

  • An Bukaci Kotu Ta Dakatar Da APC Daga Sauya Masari A Matsayin Abokin Takarar Tinubu
  • Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan

Malam Tukur Mamu, wanda babban mai shiga tsakani don ganin an sako fasinjojin da aka yi garkuwa da su a cikin jirgin kasa  Abuja zuwa Kaduna.

Mamu ya ce kafin kai harin, ya shaida wa jami’an sirri tare da hukumomi yiwuwar kai hari  amma sun kasa daukar mataki.

LEADERSHIP ta ruwaito yadda ‘yan ta’addan suka saki Manajan-Daraktan Bankin Manoma da wata mai ciki, daga bisani kuma suka sake sakin wasu mutane 11 da suka sace a cikin jirgin.

Labarai Masu Nasaba

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Tun daga wancan lokacin ‘yan ta’addan sun sha gargadin gwamnatin tarayya kan kin biyan bukatarsu tare da saurarensu, wanda ya sa suka fara barazanar kashe ragowar fasinjojin da ke hannunsu.

Da yake martani kan harin gidan yarin na Kuje, Mamu wanda hadimin Sheikh Gumi a kafafen watsa labarai, ya ce yana dab da daina shiga tsakani don sansanci tsakanin ‘yan ta’addan da gwamnatin tarayya, sakamakon halin ko in kula da gwamnatin ke nunawa a cewarsa.

Mamu ya ce rayuwarsa tana cikin hatsari, kuma idan wani abu ya same shi kada a zargi ‘yan ta’addan face tsarin shugabancin kasar nan.

Idan ba a manta ba Sheikh Ahmad Gumi ya yi gwagwarmaya a baya, don ganin ‘yan bindiga da suka addabi jihohin Kaduna, Neja, Zamfara da Sakkwato sun ajiye makamai tare da saduda.

Sai dai wasu daga tsagin gwamnati musamman ta jihar Kaduna, sun zargi shehun malamin da goya wa ‘yan bindigar baya wajen kai hare-hare.

Harin gidan yarin Kuje, ya bar baya da kura, inda dubban ‘yan Nijeriya ke tofa albarkacin bakinsu game da harin tare da kiran gwamnati ta kawo karshen tasirin ‘yan ta’adda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAbujaAnsaruHariKadunaKureMalam MamuSheikh Gumi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bukaci Kotu Ta Dakatar Da APC Daga Sauya Masari A Matsayin Abokin Takarar Tinubu

Next Post

Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

Related

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
Manyan Labarai

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

2 hours ago
Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

6 hours ago
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
Labarai

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

7 hours ago
Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

9 hours ago
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

10 hours ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

11 hours ago
Next Post
Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu

August 15, 2025
UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

August 15, 2025
Firaministan Sin Ya Bukaci A Zage Damtse Wajen Bude Sabon Babin Gina Wayewar Kai Ta Fuskar Kare Muhallin Halittu A Sabon Zamani

Firaministan Sin Ya Bukaci A Zage Damtse Wajen Bude Sabon Babin Gina Wayewar Kai Ta Fuskar Kare Muhallin Halittu A Sabon Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Katsina Za Ta Samu Kudaden Bunkasa Ilimi

Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari

August 15, 2025
Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

August 15, 2025
An Biya Falcons Duk KuÉ—in Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons

An Biya Falcons Duk KuÉ—in Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons

August 15, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (6)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (6)

August 15, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 15, 2025
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

August 15, 2025
Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.