ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Suka Kai Harin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ne Suka Kai Harin Kuje – Hadimin Gumi

by Sadiq
4 years ago
Kuje

Hadimin fitaccen Malamin addinin musulunci da ke Jihar Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, Malam Tukur Mamu, ya ce wadanda suka kai hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ne suka kai hari kan gidan yarin Kuje da ke Abuja ne.

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru da ta kai hari tare da yin garkuwa da fasinjoji a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga watan Maris, ta dauki alhakin kai hari gidan yarin Kuje da ke birnin tarayya Abuja, a daren ranar Talata.

  • An Bukaci Kotu Ta Dakatar Da APC Daga Sauya Masari A Matsayin Abokin Takarar Tinubu
  • Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan

Malam Tukur Mamu, wanda babban mai shiga tsakani don ganin an sako fasinjojin da aka yi garkuwa da su a cikin jirgin kasa  Abuja zuwa Kaduna.

ADVERTISEMENT

Mamu ya ce kafin kai harin, ya shaida wa jami’an sirri tare da hukumomi yiwuwar kai hari  amma sun kasa daukar mataki.

LEADERSHIP ta ruwaito yadda ‘yan ta’addan suka saki Manajan-Daraktan Bankin Manoma da wata mai ciki, daga bisani kuma suka sake sakin wasu mutane 11 da suka sace a cikin jirgin.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tun daga wancan lokacin ‘yan ta’addan sun sha gargadin gwamnatin tarayya kan kin biyan bukatarsu tare da saurarensu, wanda ya sa suka fara barazanar kashe ragowar fasinjojin da ke hannunsu.

Da yake martani kan harin gidan yarin na Kuje, Mamu wanda hadimin Sheikh Gumi a kafafen watsa labarai, ya ce yana dab da daina shiga tsakani don sansanci tsakanin ‘yan ta’addan da gwamnatin tarayya, sakamakon halin ko in kula da gwamnatin ke nunawa a cewarsa.

Mamu ya ce rayuwarsa tana cikin hatsari, kuma idan wani abu ya same shi kada a zargi ‘yan ta’addan face tsarin shugabancin kasar nan.

Idan ba a manta ba Sheikh Ahmad Gumi ya yi gwagwarmaya a baya, don ganin ‘yan bindiga da suka addabi jihohin Kaduna, Neja, Zamfara da Sakkwato sun ajiye makamai tare da saduda.

Sai dai wasu daga tsagin gwamnati musamman ta jihar Kaduna, sun zargi shehun malamin da goya wa ‘yan bindigar baya wajen kai hare-hare.

Harin gidan yarin Kuje, ya bar baya da kura, inda dubban ‘yan Nijeriya ke tofa albarkacin bakinsu game da harin tare da kiran gwamnati ta kawo karshen tasirin ‘yan ta’adda.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.