ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Suka Kai Harin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ne Suka Kai Harin Kuje – Hadimin Gumi

by Sadiq
4 years ago
Kuje

Hadimin fitaccen Malamin addinin musulunci da ke Jihar Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, Malam Tukur Mamu, ya ce wadanda suka kai hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ne suka kai hari kan gidan yarin Kuje da ke Abuja ne.

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru da ta kai hari tare da yin garkuwa da fasinjoji a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga watan Maris, ta dauki alhakin kai hari gidan yarin Kuje da ke birnin tarayya Abuja, a daren ranar Talata.

  • An Bukaci Kotu Ta Dakatar Da APC Daga Sauya Masari A Matsayin Abokin Takarar Tinubu
  • Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan

Malam Tukur Mamu, wanda babban mai shiga tsakani don ganin an sako fasinjojin da aka yi garkuwa da su a cikin jirgin kasa  Abuja zuwa Kaduna.

ADVERTISEMENT

Mamu ya ce kafin kai harin, ya shaida wa jami’an sirri tare da hukumomi yiwuwar kai hari  amma sun kasa daukar mataki.

LEADERSHIP ta ruwaito yadda ‘yan ta’addan suka saki Manajan-Daraktan Bankin Manoma da wata mai ciki, daga bisani kuma suka sake sakin wasu mutane 11 da suka sace a cikin jirgin.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Tun daga wancan lokacin ‘yan ta’addan sun sha gargadin gwamnatin tarayya kan kin biyan bukatarsu tare da saurarensu, wanda ya sa suka fara barazanar kashe ragowar fasinjojin da ke hannunsu.

Da yake martani kan harin gidan yarin na Kuje, Mamu wanda hadimin Sheikh Gumi a kafafen watsa labarai, ya ce yana dab da daina shiga tsakani don sansanci tsakanin ‘yan ta’addan da gwamnatin tarayya, sakamakon halin ko in kula da gwamnatin ke nunawa a cewarsa.

Mamu ya ce rayuwarsa tana cikin hatsari, kuma idan wani abu ya same shi kada a zargi ‘yan ta’addan face tsarin shugabancin kasar nan.

Idan ba a manta ba Sheikh Ahmad Gumi ya yi gwagwarmaya a baya, don ganin ‘yan bindiga da suka addabi jihohin Kaduna, Neja, Zamfara da Sakkwato sun ajiye makamai tare da saduda.

Sai dai wasu daga tsagin gwamnati musamman ta jihar Kaduna, sun zargi shehun malamin da goya wa ‘yan bindigar baya wajen kai hare-hare.

Harin gidan yarin Kuje, ya bar baya da kura, inda dubban ‘yan Nijeriya ke tofa albarkacin bakinsu game da harin tare da kiran gwamnati ta kawo karshen tasirin ‘yan ta’adda.

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

LABARAI MASU NASABA

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.