• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Suka Kai Harin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ne Suka Kai Harin Kuje – Hadimin Gumi

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Wanda Suka Kai Harin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ne Suka Kai Harin Kuje – Hadimin Gumi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hadimin fitaccen Malamin addinin musulunci da ke Jihar Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, Malam Tukur Mamu, ya ce wadanda suka kai hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ne suka kai hari kan gidan yarin Kuje da ke Abuja ne.

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru da ta kai hari tare da yin garkuwa da fasinjoji a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga watan Maris, ta dauki alhakin kai hari gidan yarin Kuje da ke birnin tarayya Abuja, a daren ranar Talata.

  • An Bukaci Kotu Ta Dakatar Da APC Daga Sauya Masari A Matsayin Abokin Takarar Tinubu
  • Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan

Malam Tukur Mamu, wanda babban mai shiga tsakani don ganin an sako fasinjojin da aka yi garkuwa da su a cikin jirgin kasa  Abuja zuwa Kaduna.

Mamu ya ce kafin kai harin, ya shaida wa jami’an sirri tare da hukumomi yiwuwar kai hari  amma sun kasa daukar mataki.

LEADERSHIP ta ruwaito yadda ‘yan ta’addan suka saki Manajan-Daraktan Bankin Manoma da wata mai ciki, daga bisani kuma suka sake sakin wasu mutane 11 da suka sace a cikin jirgin.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Tun daga wancan lokacin ‘yan ta’addan sun sha gargadin gwamnatin tarayya kan kin biyan bukatarsu tare da saurarensu, wanda ya sa suka fara barazanar kashe ragowar fasinjojin da ke hannunsu.

Da yake martani kan harin gidan yarin na Kuje, Mamu wanda hadimin Sheikh Gumi a kafafen watsa labarai, ya ce yana dab da daina shiga tsakani don sansanci tsakanin ‘yan ta’addan da gwamnatin tarayya, sakamakon halin ko in kula da gwamnatin ke nunawa a cewarsa.

Mamu ya ce rayuwarsa tana cikin hatsari, kuma idan wani abu ya same shi kada a zargi ‘yan ta’addan face tsarin shugabancin kasar nan.

Idan ba a manta ba Sheikh Ahmad Gumi ya yi gwagwarmaya a baya, don ganin ‘yan bindiga da suka addabi jihohin Kaduna, Neja, Zamfara da Sakkwato sun ajiye makamai tare da saduda.

Sai dai wasu daga tsagin gwamnati musamman ta jihar Kaduna, sun zargi shehun malamin da goya wa ‘yan bindigar baya wajen kai hare-hare.

Harin gidan yarin Kuje, ya bar baya da kura, inda dubban ‘yan Nijeriya ke tofa albarkacin bakinsu game da harin tare da kiran gwamnati ta kawo karshen tasirin ‘yan ta’adda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAbujaAnsaruHariKadunaKureMalam MamuSheikh Gumi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bukaci Kotu Ta Dakatar Da APC Daga Sauya Masari A Matsayin Abokin Takarar Tinubu

Next Post

Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

Related

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

1 day ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

1 day ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 day ago
Next Post
Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

Sin: Kalamam Blinken Kan Kasar Sin Take Gaskiya Ne Da Neman Mayar Da Fari Baki

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.