ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Mauricio

A cikin wannan satin ne kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta nada Mauricio Pochet-tino a matsayin sabon kociyanta, wanda zai fara aiki ranar 1 ga watan Yulin wannan shekarar ta 2023.

Kungiyar ta dauki tsohon kocin Tottenham, bayan da ta kammala kakar Premier League ta bana a mataki na 12 kuma mataki mafi muni da kungiyar ta taba tsintar kan-ta sama da shekara 37.

Wanene Pochettino?
Espanyol
Lokacin da yake koyar da kungiyar kwallon kafa ta Espanyol ya jagoranci kungiyar ta kasar Sipaniya adadin wasanni 161 inda ya ci wasanni 53 da canjaras 38 aka doke shi 70. Bayan da Pochetino ya yi ritaya daga buga wa Espanyol wasa a shekarar 2006, dan kasar Argentina ya karbi aikin jan ragamar kungiyar a watan Janairun shekara ta 2009 a lokacin da kungiyar ke fuskantar barin La Liga.

ADVERTISEMENT

Daga nan ya ceto kungiyar wadda ta kare a tsakiyar teburi – wanda ya ci Barcelona a gasar La Liga da yin canjaras da kungiyar ta a gasar Copa del Rey sannan a kakar wasa ukun da ya ja ragamar Espanyol ta yi ta 11 da ta takwas da kuma ta 14, amma ya bar kungiyar tana cikin ‘yan karshen teburi cikin watan Nuwamba lokacin tana fuskan-tar barazanar tattalin arziki.

Southampton
Bayan da ya koma kasar Ingila da koyarwa, Pochettino ya ci wasanni 23 da canjaras 18 aka doke shi fafatawa 79 bayan da ya karbi aikin horar da Southampton a tsakiyar kaka, bayan da ya maye gurbin Nigel Adkins.
Kocin ya ja ragamar kungiyar ta kammala Premier a mataki na 14 a teburi, sannan a kaka ta gaba Southampton ta yi ta takwas sai dai Pochettino ya yi aikin a lokacin da baya jin turaci, inda ya dauki mai yi masa fassara a lokacin ganawa da ‘yan jarida, am-ma hakan bai hana shi samun nasara ba a Ingila.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Tottenham
Mai koyarwa Pochetino ya samu nasarar lashe wasanni 159 da canjaras 62 aka doke shi 72 sannan a shekara biyar da Pochettino ya yi a Tottenham, kungiyar ta samu na-sara mai yawa a tarihin kafuwarta.
Tottenham ta fara kare kakar Premier League a mataki na biyar da na uku da na biyu da sake yin na uku, sannan ta kammala a ta biyar a teburin babbar gasar firimiya ta Ingila.

Haka kuma a karkashin Pochetino,Tottenham ta kai karawar karshe a Champions League da kuma League Cup sai dai ya hada matasan ‘yan wasa a Tottenham a loka-cin da kungiyar ta yi ta biyu a Premier a kakar 2016 zuwa 2017.

Saboda ya hada ‘yan wasa daga Ingila da suka hada da Harry Kane da Dele Alli da kuma Eric Dier, sannan ya hada da wasu daga waje da suka hada da Christian Eriksen da Son Heung-min da kuma Toby Alderweireld. Tottenham ta dauki masu ko-yarwa 10 a cikin shekara 12 kafin ta dauki Pochettino a 2014 sai dai tun bayan da ta sallami kocin a Nuwambar 2019 daga nan ne abubuwa suka sake komawa baya, inda ta dauki Jose Mourinho da Ryan Mason na rikon kwarya har karo biyu da Nuno Espiri-to Santo da Antonio Conte da na rikon kwarya Cristian Stellini.

Duk da haka Tottenham, wadda ta buga Champions League a bana ta kasa samun gurbin shiga gasar zakarun Turai ta badi, bayan da ita ce ta takwas da maki 60 a kakar bana.

Paris St Germain(PSG)
A zaman da yayi a kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German ya ci wasanni 55 da canjaras 15 aka doke shi wasa 14 sannan ya buga wa Paris St-Germain wasa tsakanin 2001 zuwa 2003, wadda ta dauke shi aikin koci a 2021.

Ya dauki babban kofi a matakinsa na mai horarwa, bayan da ya lashe Coupe de France a kakar 2020 zuwa 2021 da kuma Ligue 1 a shekarar 2021 zuwa 2022 sai dai a kakar 2020 zuwa 2021 PSG ta kare a mataki na biyu, bayan da Lille ta dauki Ligue 1, sannan PSG ta kasa kai wa wasan karshe a Champions League.

Karo na biyu kenan da ta kasa cin babban kofin Faransa a kaka tara, hakan ya sa aka kori Pochettino bayan ya maye gurbin Thomas Tuchel a PSG, lokacin da dan kasar Jamus din ya koma Chelsea, inda ya maye gurbin Frank Lampard.

Mauricio
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.