ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

by Rabilu Sanusi Bena
11 months ago
Sadau

Abba Sadau, ‘ya’yan fitacciyar jaruma Rahama Sadau, ya bayyana alhini kan rasuwar mahaifinsu, Alhaji Ibrahim Sadau, wanda ya kwanta dama a ranar 22 ga watan Yunin da ya gabata, mahaifin nasu dai; ya rasu ne da sanyin safiyar ranar Talata, kwana daya bayan dawowarsa daga aikin Hajji, ya rasu a asibitin sojoji na 44, da ke Jihar Kaduna da misalin karfe 4:00 na asuba, sanadiyar ciwon Siga.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa, an yi jana’idarsa da misalin karfe 10:00 na safiyar ranar da ya rasu, a harabar wata makarantar Islamiyya da ke kusa da gidansa, a kan titin Lome da ke Unguwar Rimi.

  • INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

Dattijon mai kimanin shekara 58, ya rasu ya bar mata biyu da ‘ya’ya tara, daga cikinsu akwai jaruma a masana’antar Kannywood, Rahama Sadau; wacce ita ce ‘yarsa ta biyu.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin ‘ya’yan mamacin, Furodusa Haruna Sadau lbrahim, wanda aka fi sani da Abba Sadau; ya bayyana irin halin kidimewa da ya shiga, sakamakon wancan rashi na mahaifin nasu. Abba, wanda furodusa ne a masana’antar Kannywood, ya ce, “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un, wannan rashi ba mu taba yin irinsa ba a danginmu baki-daya, wannan shi ne karo na farko da muka yi irin wannan rashi babba.

“Wannan rashi ya yi matukar taba mu, ya taba kowa da kowa. Domin kuuwa, ni har yanzu ban gama yarda cewa ya mutu ba; bayan dawowarsa daga Saudiyya, ya ce; ba shi da lafiya, daga nan sai ya kira ni a waya ya ce da ni na turo masa likita, sai na ce da shi; kamata ya yi ya je asibiti a duba shi sosai, ana kai shi asibitin, sai labari ya canza; jikin nasa ya yi tsanani sosai”, in ji Abba.

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Sadau, ya ci gaba da bayyana yadda zai ci gaba rika tunawa da mahaifin nasu, inda ya ce; “Akwai abubuwa da dama da zan rika tuna mahaifina da su, amma abin da zan fi tunawa da shi, wanda kuma zan yi koyi da su shi ne kula da ibada, domin ba za a taba zuwa masallaci ka gan shi a sahu na biyu ba, koda-yaushe a sahun farko za ka gan shi. In dai ibada ce, a gaba za ka gan shi; an shaide shi da haka”, in ji shi.

“Ina godiya ga yan Kannywood da sauran al’ummar da suka halarci jana’iza, wallahi har kwalla na yi saboda irin dandazon jama’a da na gani, Allah ya saka wa kowa da alhairi, sannan kuma ya ba mu hakurin rashin wannan mahaifi namu, muna fatan yadda ya samu kyakkyawar shaida a wajen mutane, ya sa ya samu wannan a can”.

Sadau
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.