• Leadership Hausa
Wednesday, December 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 

by CMG Hausa
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asabar din nan ne, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin JKS Wang Yi ya gana da ministar harkokin wajen kasar Jamus Annalena Baerbock a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da martaba manufar harkokin waje mai cin gashin kanta, da tabbatar da bin dabarun bude kofa na samun moriyar juna da cimma nasara tare, da kiyaye ikon MDD da tsarin kasa da kasa da aka kafa bayan yakin duniya na biyu. Wang Yi ya kara bayyana cewa, kasar Sin na son karfafa cudanya da mu’amala da kasar Jamus domin inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata.

  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

A nata bangare, Baerbock ta ce, kasancewar kasar Sin mambar dindindin a kwamitin sulhu na MDD, kuma kasar Jamus babbar kasa a nahiyar Turai, yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su karfafa tattaunawa da mu’amala. Kuma kasarta na martaba manufar Sin daya tak a duniya.

Baya ga haka, a jiya ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya gudanar da taron tattaunawa kan harkokin diplomasiyya da tsaro karo na shida tsakanin kasar Sin da Jamus tare da takwararsa ta kasar ta Jamus Baerbock a nan birnin Beijing.

Wang yi
Wang Yi

A yayin taron, Qin Gang ya ce, kasashen Sin da Jamus abokan hadin gwiwa ne ba abokan gaba ba, kuma ya kamata sassan biyu su bunkasa dangantakarsu da kansu. Kasar Sin tana son yin mu’amala da kasar Jamus tare da inganta hadin gwiwa a dukkan fannoni.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

Sai Da Ruwan Ciki Ake Jan Na Rijiya

A nata bangare, Baerbock ta bayyana cewa, kasar Jamus na ci gaba da raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin cikin ‘yanci, kuma tana fatan dawo da mu’amala da tattaunawa a fannoni daban-daban a tsakanin kasashen biyu cikin sauri. Ban da wannan kuma, bangaren Jamus yana mai da hankali sosai kan kiyaye tsarin samar da kayayyaki, bai amince da “mayar da wani bangare saniyar ware a fannin tattalin arziki” ba, kuma yana tsayawa tsayin dak kan nuna daidaito ga kamfanonin juna. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsakanin Samari Da ‘Yan Mata, Wa Ya Kamata Ya Ba Wani ‘Ramadan Basket’

Next Post

Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Related

Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

1 min ago
Sai Da Ruwan Ciki Ake Jan Na Rijiya
Daga Birnin Sin

Sai Da Ruwan Ciki Ake Jan Na Rijiya

1 hour ago
Kasar Sin Za Ta Soke Harajin Kwastam Da Ta Buga Kan Kaso 98% Na Hajojin Wasu Kasashen Afirka 6
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Soke Harajin Kwastam Da Ta Buga Kan Kaso 98% Na Hajojin Wasu Kasashen Afirka 6

2 hours ago
An Yabawa Sin Kan Taimakon Ilimi Ga Dalibai Masu Rauni A Habasha 
Daga Birnin Sin

An Yabawa Sin Kan Taimakon Ilimi Ga Dalibai Masu Rauni A Habasha 

2 hours ago
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Gwajin Fasahar Intanet Na Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Gwajin Fasahar Intanet Na Tauraron Dan Adam

5 hours ago
Madagascar
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Ya Taya Takwaransa Na Madagascar Murnar Lashe Zabe

5 hours ago
Next Post
Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

December 6, 2023
Sai Da Ruwan Ciki Ake Jan Na Rijiya

Sai Da Ruwan Ciki Ake Jan Na Rijiya

December 6, 2023
Kasar Sin Za Ta Soke Harajin Kwastam Da Ta Buga Kan Kaso 98% Na Hajojin Wasu Kasashen Afirka 6

Kasar Sin Za Ta Soke Harajin Kwastam Da Ta Buga Kan Kaso 98% Na Hajojin Wasu Kasashen Afirka 6

December 6, 2023
Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 

Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 

December 6, 2023
An Yabawa Sin Kan Taimakon Ilimi Ga Dalibai Masu Rauni A Habasha 

An Yabawa Sin Kan Taimakon Ilimi Ga Dalibai Masu Rauni A Habasha 

December 6, 2023
Sojoji

Dalilin Da Yasa Ta’addanci Ke Ci Gaba Duk Da Kasafin Kudi Mai Gwabi Da Sojoji Ke Samu – Shugaban Tsaro

December 6, 2023
Rashin tsaro

Rashin Tsaro: Kungiyoyi Sun Yi Zanga-zanga, Sun Bukaci Ministan Tsaro Ya Yi Murabus

December 6, 2023
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Gwajin Fasahar Intanet Na Tauraron Dan Adam

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Gwajin Fasahar Intanet Na Tauraron Dan Adam

December 6, 2023
Madagascar

Shugaban Kasar Sin Ya Taya Takwaransa Na Madagascar Murnar Lashe Zabe

December 6, 2023
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

‘Yansandan Sun Kama Masu Laifi 130 A Watan Nuwamba A Katsina

December 6, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.