ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
Wang yi

Wang Yi, darektan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a yau Litinin a nan birnin Beijing, inda ya yi kira da a yi kokarin gyara dangantakar kasashen Sin da Amurka wadda ta yi tsami.

Wang ya ce ziyarar ta Blinken a nan Beijing ta zo ne a wani muhimmin lokaci a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, inda ake bukatar zabi tsakanin tattaunawa ko gwabzawa, hadin gwiwa ko rikici.

  • Ministan Harkokin Kasuwanci na Sin Wang Wentao Ya Gana Da Darakta Janar Ta WTO Ngozi Okonjo-Iweala

Lura da cewa lokaci na tafiya haka ma alakar dake tsakanin Sin da Amurka. Wang ya ce canza tarihi ba zai yi tasiri ga makoma ba, haka ma wargaza dangantakar dake tsakanin kasashen biyu don a sake gina sabuwa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dole ne mu nuna kyakkyawar hali ga jama’a, da tarihi da kuma duniya baki daya, tare da gyara dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka.” Ya yi kira ga bangarorin biyu da su maido da huldar da ke tsakanin kasashen biyu zuwa tafarkin da ya dace, da kuma samar da hanya madaidaiciya ga Sin da Amurka don samun jituwa a sabon zamani.

A jiya ne, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Qin Gang ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken dake ziyara a nan birnin Beijing.

LABARAI MASU NASABA

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

A yayin shawarwarin, Qin Gang ya bayyana cewa, yanzu dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala mafi tsanani bayan da kasashen biyu suka kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu, wannan bai dace da moriyar jama’ar kasashen biyu da begen kasa da kasa ba. Sin tana yin kokarin raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Amurka ta zaman lafiya da amfani, Sin tana fatan kasar Amurka za ta maida hankali ga kasar Sin bisa hakikanin yanayi, da yin kokari tare da kasar Sin, da tabbatar da tushen siyasa na raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da daidaita matsaloli ba zato ba tsammani cikin lumana yadda ya kamata. Kana kasashen biyu ya kamata su aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali, da sa kaimi ga maido da dangantakarsu.

Qin Gang ya bayyana matsayin kasar Sin kan manyan batutuwan dake shafar moriyar kasar Sin, ciki har da batun yankin Taiwan, ya kalubalanci bangaren kasar Amurka da ya bi ka’idar Sin daya tak a duniya da hadaddun rahotanni uku da Sin da Amurka suka daddale, da cika alkawarinta na kin amincewa da ‘yancin yankin Taiwan.

Hakazalika kuma, bangarorin biyu sun zurfafa mu’amala da juna kan yadda za a raya dangantakar dake tsakaninsu da manyan batutuwan da abin ya shafa. (Mai Fassarawa: Zainab Zhang&Yahaya Babs)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Next Post
Wang yi

Tinubu Ya Kori Shugabannin Gudanarwar Ma'aikatu Da Hukumomin Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.