• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

by CMG Hausa
2 years ago
wang yi

Babban jami’in diflomasiyyar kasar Sin Wang Yi, ya bayyana cewa, kamata ya yi Amurka ta dauki kwararan matakai don dawo da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka kan hanyar da ta dace.

Wang, daraktan ofishin hukumar kula da harkokin wajen na kwamitin kolin JKS ya bayyana hakan ne jiya Alhamis, yayin ganawarsa da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a gefen taron ministocin harkokin wajen kungiyar ASEAN. Yana mai cewa, bangarorin biyu sun cimma matsaya ta hanyar zurfafa tattaunawa ta gaskiya, yayin ziyarar da Blinken ya kawo kasar Sin a watan da ya gabata.

  • Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ya kara da cewa, muhimmiyar yarjejeniya ita ce komawa kan ajandar da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, da daukar muhimmin mataki na tsara tsarin da ya dace wajen inganta alakar manyan kasashen biyu

Wang ya yi karin haske kan matsayar kasar Sin game da batun yankin Taiwan, inda ya bukaci Amurka da ta guji tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin ba gaira ba dalili, ko kuma yin zagon kasa ga ikon mulkinta da ma cikakkun yankunanta, da dakatar da dakile ci gabanta ta fuskar tattalin arziki, da cinikayya, da harkokin kimiyya da fasaha, da mayar da kasar Sin saniyar ware, kana ta cire dukkan takunkumai na babu gaira babu dalili da ta kakkaba mata.

Game da wannan ganawa, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a yau cewa, Wang Yi ya bayyana matsayin Sin kan tsaron yanar gizo da yaki da miyagun kwayoyi a yayin ganawar.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wang Wenbin ya kara da cewa, kasar Sin tana tinkarar hare-hare ta yanar gizo da ake kai wa hukumominta a kowace rana, kuma yawancinsu daga Amurka. Ya ce Sin kasa ce da ta fi fama da hare-hare ta yanar gizo, don haka, bai kamata Amurka ta zarge ta kan wannan batu ba.

Ban da wannan kuma, Wang ya ce, Sin da Amurka sun yi tattaunawa kan batun maganin Fentanyl a yayin ganawar, inda Sin ta bayyana matsayinta da damuwarta. Wang Yi ya yi nuni da cewa, Sin ta fi tsayawa tsayin daka kan manufar yaki da miyagun kwayoyi a duniya, amma Amurka ba ta amince da kokarin Sin a wannan fanni ba, tana zargin Sin da amfani da irin maganin, da kuma kama mutanen Sin ba bisa doka ba. Ya ce ya kamata Amurka ta daidaita batun bisa yanayin na adalci da girmamawa da hadin gwiwa, da soke takunkumin da ta sakawa hukumomin Sin masu kula da ayyukan yaki da miyagun kwayoyi cikin hanzari, don kawar da cikas ga shawarwari da hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu. (Ibrahim Yaya, Zainab)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al’ummar Laos A Rikicin Ukraine?

Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al'ummar Laos A Rikicin Ukraine?

LABARAI MASU NASABA

wang yi

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.