• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban jami’in diflomasiyyar kasar Sin Wang Yi, ya bayyana cewa, kamata ya yi Amurka ta dauki kwararan matakai don dawo da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka kan hanyar da ta dace.

Wang, daraktan ofishin hukumar kula da harkokin wajen na kwamitin kolin JKS ya bayyana hakan ne jiya Alhamis, yayin ganawarsa da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a gefen taron ministocin harkokin wajen kungiyar ASEAN. Yana mai cewa, bangarorin biyu sun cimma matsaya ta hanyar zurfafa tattaunawa ta gaskiya, yayin ziyarar da Blinken ya kawo kasar Sin a watan da ya gabata.

  • Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ya kara da cewa, muhimmiyar yarjejeniya ita ce komawa kan ajandar da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, da daukar muhimmin mataki na tsara tsarin da ya dace wajen inganta alakar manyan kasashen biyu

Wang ya yi karin haske kan matsayar kasar Sin game da batun yankin Taiwan, inda ya bukaci Amurka da ta guji tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin ba gaira ba dalili, ko kuma yin zagon kasa ga ikon mulkinta da ma cikakkun yankunanta, da dakatar da dakile ci gabanta ta fuskar tattalin arziki, da cinikayya, da harkokin kimiyya da fasaha, da mayar da kasar Sin saniyar ware, kana ta cire dukkan takunkumai na babu gaira babu dalili da ta kakkaba mata.

Game da wannan ganawa, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a yau cewa, Wang Yi ya bayyana matsayin Sin kan tsaron yanar gizo da yaki da miyagun kwayoyi a yayin ganawar.

Labarai Masu Nasaba

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Wang Wenbin ya kara da cewa, kasar Sin tana tinkarar hare-hare ta yanar gizo da ake kai wa hukumominta a kowace rana, kuma yawancinsu daga Amurka. Ya ce Sin kasa ce da ta fi fama da hare-hare ta yanar gizo, don haka, bai kamata Amurka ta zarge ta kan wannan batu ba.

Ban da wannan kuma, Wang ya ce, Sin da Amurka sun yi tattaunawa kan batun maganin Fentanyl a yayin ganawar, inda Sin ta bayyana matsayinta da damuwarta. Wang Yi ya yi nuni da cewa, Sin ta fi tsayawa tsayin daka kan manufar yaki da miyagun kwayoyi a duniya, amma Amurka ba ta amince da kokarin Sin a wannan fanni ba, tana zargin Sin da amfani da irin maganin, da kuma kama mutanen Sin ba bisa doka ba. Ya ce ya kamata Amurka ta daidaita batun bisa yanayin na adalci da girmamawa da hadin gwiwa, da soke takunkumin da ta sakawa hukumomin Sin masu kula da ayyukan yaki da miyagun kwayoyi cikin hanzari, don kawar da cikas ga shawarwari da hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu. (Ibrahim Yaya, Zainab)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?

Next Post

Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al’ummar Laos A Rikicin Ukraine?

Related

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

7 hours ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

9 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

9 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

21 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

22 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

23 hours ago
Next Post
Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al’ummar Laos A Rikicin Ukraine?

Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al'ummar Laos A Rikicin Ukraine?

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.