• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban jami’in diflomasiyyar kasar Sin Wang Yi, ya bayyana cewa, kamata ya yi Amurka ta dauki kwararan matakai don dawo da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka kan hanyar da ta dace.

Wang, daraktan ofishin hukumar kula da harkokin wajen na kwamitin kolin JKS ya bayyana hakan ne jiya Alhamis, yayin ganawarsa da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a gefen taron ministocin harkokin wajen kungiyar ASEAN. Yana mai cewa, bangarorin biyu sun cimma matsaya ta hanyar zurfafa tattaunawa ta gaskiya, yayin ziyarar da Blinken ya kawo kasar Sin a watan da ya gabata.

  • Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ya kara da cewa, muhimmiyar yarjejeniya ita ce komawa kan ajandar da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, da daukar muhimmin mataki na tsara tsarin da ya dace wajen inganta alakar manyan kasashen biyu

Wang ya yi karin haske kan matsayar kasar Sin game da batun yankin Taiwan, inda ya bukaci Amurka da ta guji tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin ba gaira ba dalili, ko kuma yin zagon kasa ga ikon mulkinta da ma cikakkun yankunanta, da dakatar da dakile ci gabanta ta fuskar tattalin arziki, da cinikayya, da harkokin kimiyya da fasaha, da mayar da kasar Sin saniyar ware, kana ta cire dukkan takunkumai na babu gaira babu dalili da ta kakkaba mata.

Game da wannan ganawa, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a yau cewa, Wang Yi ya bayyana matsayin Sin kan tsaron yanar gizo da yaki da miyagun kwayoyi a yayin ganawar.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Wenbin ya kara da cewa, kasar Sin tana tinkarar hare-hare ta yanar gizo da ake kai wa hukumominta a kowace rana, kuma yawancinsu daga Amurka. Ya ce Sin kasa ce da ta fi fama da hare-hare ta yanar gizo, don haka, bai kamata Amurka ta zarge ta kan wannan batu ba.

Ban da wannan kuma, Wang ya ce, Sin da Amurka sun yi tattaunawa kan batun maganin Fentanyl a yayin ganawar, inda Sin ta bayyana matsayinta da damuwarta. Wang Yi ya yi nuni da cewa, Sin ta fi tsayawa tsayin daka kan manufar yaki da miyagun kwayoyi a duniya, amma Amurka ba ta amince da kokarin Sin a wannan fanni ba, tana zargin Sin da amfani da irin maganin, da kuma kama mutanen Sin ba bisa doka ba. Ya ce ya kamata Amurka ta daidaita batun bisa yanayin na adalci da girmamawa da hadin gwiwa, da soke takunkumin da ta sakawa hukumomin Sin masu kula da ayyukan yaki da miyagun kwayoyi cikin hanzari, don kawar da cikas ga shawarwari da hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu. (Ibrahim Yaya, Zainab)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?

Next Post

Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al’ummar Laos A Rikicin Ukraine?

Related

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

10 hours ago
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

11 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

12 hours ago
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

13 hours ago
An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO
Daga Birnin Sin

An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO

15 hours ago
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

1 day ago
Next Post
Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al’ummar Laos A Rikicin Ukraine?

Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al'ummar Laos A Rikicin Ukraine?

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.