• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Wang Yi

Ran 15 ga wata bisa agogon wurin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden a rukunin gidajen alfarma na Filoli dake birnin San Francisco na kasar Amurka. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi wa manema labarai bayyani bayan taron.

 

Ya ce, ban da ganawar da shugabnanin biyu za su yi yayin taron APEC, shugaba Joe Biden ya gayyaci shugaba Xi Jinping don ganawa ta musamman a tsakaninsu a wannan karo, kuma shugabannin biyu sun tattauna yadda ya kamata. Ana iya cewa, wannan ganawa na da ma’ana da muhimmanci matuka.

  • Yanzu-yanzu: Kotun Daukaka Kara Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Gwamnan Kano Gobe A Abuja
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Ban da wannan kuma, ya ce, shugabannin biyu sun gana a wani muhimmin lokaci na huldar kasashen biyu. Kasashen duniya na matukar bukatar huldar kasashen biyu mai inganci. Ganawar ta wannan karo ta aza wani tubali mai kyau ga dangantakar kasashen biyu da ma abu mai muhimmanci ga huldar kasashen duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

An shafe sa’o’i 4 ana gudanar da wannan ganawa, inda shugabannin biyu suka yi musanyar ra’ayoyi mai zurfi da ba da shawara kan yadda bangarorin biyu za su cimma ra’ayi na gaskiya da daidaita bambanci da ingiza hadin kai da shawarwari tsakaninsu, tattaunawar da suka yi ya shafi rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila da rikicin Ukraine da sauyin yanayi da na’urori masu sarrafa kansu da dai sauransu. Kazalika sun tabbatar da nauyin dake wuyansu a duniya da samar da makomar hadin kai.

Wang Yi

Dadin dadawa, Wang Yi ya ce, a yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya gabatar da matsayin da Sin ta dade take dauka kan huldar dake tsakaninsu. Wato Sin da Amurka abokan juna ne, ya kamata kasashen biyu sun hada kansu kan bangarorin da suka dace da muradunsu, yana mai fatan Amurka za ta zabi hanyar da ta dace don bunkasa huldarsu yadda ya kamata.

 

Na biyu, mutunta juna da zama tare cikin lumana da hadin kai da cin moriya tare.

 

Na uku, Sin da Amurka su cimma matsaya daya kan dangantakarsu, don daidaita mabambancin ra’ayi tsakaninsu da ciyar da hadin kansu gaba da sauke nauyin dake wuyansu tare da ingiza mu’ammala a fannin al’adu tsakaninsu.

 

Sannan, a yayin wani taron manema labarai da aka shirya a yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Mao Ning ta bayyana cewa, shugaba Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden sun yj tattaunawar keke da keke mai zurfi a jiya Laraba, kuma hanyar da ta dace da kyautata dangantakarsu, ta kara fayyace nauyin dake wuyan manyan kasashen tare da samar da “burin San Francisco” domin kyautata makomarsu.

 

A cewar Mao Ning, wannan kyakkyawar ganawa ce mai ma’ana dake da muhimmiyar tasiri mai kyau. Tana mai cewa, batu ne mai muhimmanci ga duniya, haka kuma nasara ce ga tarihin dangantakar kasashen biyu.

 

Mao Ning ta jaddada cewa, tattaunawa da hadin gwiwa ita ce kadai zabi mai kyau ga kasashen biyu. Kuma ya kamata tattaunawar ta San Francisco ta zama mafarin kyautata dangantakarsu. Bugu da kari, akwai bukatar bangarorin biyu su karfafa tubalin dangantakarsu, da gina ginshikin hulda da juna cikin aminci da karko kuma bisa alkibla mai dorewa. (Masu Fassarawa: Amina Xu, Faiza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.