ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Wang Yi

Ran 15 ga wata bisa agogon wurin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden a rukunin gidajen alfarma na Filoli dake birnin San Francisco na kasar Amurka. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi wa manema labarai bayyani bayan taron.

 

Ya ce, ban da ganawar da shugabnanin biyu za su yi yayin taron APEC, shugaba Joe Biden ya gayyaci shugaba Xi Jinping don ganawa ta musamman a tsakaninsu a wannan karo, kuma shugabannin biyu sun tattauna yadda ya kamata. Ana iya cewa, wannan ganawa na da ma’ana da muhimmanci matuka.

ADVERTISEMENT
  • Yanzu-yanzu: Kotun Daukaka Kara Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Gwamnan Kano Gobe A Abuja
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Ban da wannan kuma, ya ce, shugabannin biyu sun gana a wani muhimmin lokaci na huldar kasashen biyu. Kasashen duniya na matukar bukatar huldar kasashen biyu mai inganci. Ganawar ta wannan karo ta aza wani tubali mai kyau ga dangantakar kasashen biyu da ma abu mai muhimmanci ga huldar kasashen duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

An shafe sa’o’i 4 ana gudanar da wannan ganawa, inda shugabannin biyu suka yi musanyar ra’ayoyi mai zurfi da ba da shawara kan yadda bangarorin biyu za su cimma ra’ayi na gaskiya da daidaita bambanci da ingiza hadin kai da shawarwari tsakaninsu, tattaunawar da suka yi ya shafi rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila da rikicin Ukraine da sauyin yanayi da na’urori masu sarrafa kansu da dai sauransu. Kazalika sun tabbatar da nauyin dake wuyansu a duniya da samar da makomar hadin kai.

Wang Yi

Dadin dadawa, Wang Yi ya ce, a yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya gabatar da matsayin da Sin ta dade take dauka kan huldar dake tsakaninsu. Wato Sin da Amurka abokan juna ne, ya kamata kasashen biyu sun hada kansu kan bangarorin da suka dace da muradunsu, yana mai fatan Amurka za ta zabi hanyar da ta dace don bunkasa huldarsu yadda ya kamata.

 

Na biyu, mutunta juna da zama tare cikin lumana da hadin kai da cin moriya tare.

 

Na uku, Sin da Amurka su cimma matsaya daya kan dangantakarsu, don daidaita mabambancin ra’ayi tsakaninsu da ciyar da hadin kansu gaba da sauke nauyin dake wuyansu tare da ingiza mu’ammala a fannin al’adu tsakaninsu.

 

Sannan, a yayin wani taron manema labarai da aka shirya a yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Mao Ning ta bayyana cewa, shugaba Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden sun yj tattaunawar keke da keke mai zurfi a jiya Laraba, kuma hanyar da ta dace da kyautata dangantakarsu, ta kara fayyace nauyin dake wuyan manyan kasashen tare da samar da “burin San Francisco” domin kyautata makomarsu.

 

A cewar Mao Ning, wannan kyakkyawar ganawa ce mai ma’ana dake da muhimmiyar tasiri mai kyau. Tana mai cewa, batu ne mai muhimmanci ga duniya, haka kuma nasara ce ga tarihin dangantakar kasashen biyu.

 

Mao Ning ta jaddada cewa, tattaunawa da hadin gwiwa ita ce kadai zabi mai kyau ga kasashen biyu. Kuma ya kamata tattaunawar ta San Francisco ta zama mafarin kyautata dangantakarsu. Bugu da kari, akwai bukatar bangarorin biyu su karfafa tubalin dangantakarsu, da gina ginshikin hulda da juna cikin aminci da karko kuma bisa alkibla mai dorewa. (Masu Fassarawa: Amina Xu, Faiza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
Next Post
Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.