ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
3 years ago
Wang Yi

Ran 15 ga wata bisa agogon wurin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden a rukunin gidajen alfarma na Filoli dake birnin San Francisco na kasar Amurka. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi wa manema labarai bayyani bayan taron.

 

Ya ce, ban da ganawar da shugabnanin biyu za su yi yayin taron APEC, shugaba Joe Biden ya gayyaci shugaba Xi Jinping don ganawa ta musamman a tsakaninsu a wannan karo, kuma shugabannin biyu sun tattauna yadda ya kamata. Ana iya cewa, wannan ganawa na da ma’ana da muhimmanci matuka.

ADVERTISEMENT
  • Yanzu-yanzu: Kotun Daukaka Kara Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Gwamnan Kano Gobe A Abuja
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Ban da wannan kuma, ya ce, shugabannin biyu sun gana a wani muhimmin lokaci na huldar kasashen biyu. Kasashen duniya na matukar bukatar huldar kasashen biyu mai inganci. Ganawar ta wannan karo ta aza wani tubali mai kyau ga dangantakar kasashen biyu da ma abu mai muhimmanci ga huldar kasashen duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

An shafe sa’o’i 4 ana gudanar da wannan ganawa, inda shugabannin biyu suka yi musanyar ra’ayoyi mai zurfi da ba da shawara kan yadda bangarorin biyu za su cimma ra’ayi na gaskiya da daidaita bambanci da ingiza hadin kai da shawarwari tsakaninsu, tattaunawar da suka yi ya shafi rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila da rikicin Ukraine da sauyin yanayi da na’urori masu sarrafa kansu da dai sauransu. Kazalika sun tabbatar da nauyin dake wuyansu a duniya da samar da makomar hadin kai.

Wang Yi

Dadin dadawa, Wang Yi ya ce, a yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya gabatar da matsayin da Sin ta dade take dauka kan huldar dake tsakaninsu. Wato Sin da Amurka abokan juna ne, ya kamata kasashen biyu sun hada kansu kan bangarorin da suka dace da muradunsu, yana mai fatan Amurka za ta zabi hanyar da ta dace don bunkasa huldarsu yadda ya kamata.

 

Na biyu, mutunta juna da zama tare cikin lumana da hadin kai da cin moriya tare.

 

Na uku, Sin da Amurka su cimma matsaya daya kan dangantakarsu, don daidaita mabambancin ra’ayi tsakaninsu da ciyar da hadin kansu gaba da sauke nauyin dake wuyansu tare da ingiza mu’ammala a fannin al’adu tsakaninsu.

 

Sannan, a yayin wani taron manema labarai da aka shirya a yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Mao Ning ta bayyana cewa, shugaba Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden sun yj tattaunawar keke da keke mai zurfi a jiya Laraba, kuma hanyar da ta dace da kyautata dangantakarsu, ta kara fayyace nauyin dake wuyan manyan kasashen tare da samar da “burin San Francisco” domin kyautata makomarsu.

 

A cewar Mao Ning, wannan kyakkyawar ganawa ce mai ma’ana dake da muhimmiyar tasiri mai kyau. Tana mai cewa, batu ne mai muhimmanci ga duniya, haka kuma nasara ce ga tarihin dangantakar kasashen biyu.

 

Mao Ning ta jaddada cewa, tattaunawa da hadin gwiwa ita ce kadai zabi mai kyau ga kasashen biyu. Kuma ya kamata tattaunawar ta San Francisco ta zama mafarin kyautata dangantakarsu. Bugu da kari, akwai bukatar bangarorin biyu su karfafa tubalin dangantakarsu, da gina ginshikin hulda da juna cikin aminci da karko kuma bisa alkibla mai dorewa. (Masu Fassarawa: Amina Xu, Faiza Mustapha)

Wang Yi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.