ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

by CGTN Hausa
3 years ago
Gona

Innocent Mojidi dan kasar Najeriya ne mai shekaru 35 da haifuwa, ya taba zuwa kasar Sin sau biyu don samun horo a fannin aikin gona, yauzu yana noman shimkafa da masara a gonakinsa dake karkarar birnin Abuja hedkwatar Najeriya. Saboda kwarewar da ya samu, ya zama masanin aikin gona a garinsu. ‘Yan Afrika da dama ne kamar Innocent Mojidi suka zo kasar Sin don koyon dabarun aikin noma na zamani, matakin da ya taimaka musu wajen tinkarar matsalar karancin isasshen hatsi.

A cikin shekaru 10 da suka gabata bayan Sin da Afrika suka yi hadin gwiwa a fannin aikin noma, Sin ta kulla yarjeniyoyi 34 da kasashen Afrika da AU da AGRA a wannan bangare, da kuma yin mu’ammala kan samar da isasshen hatsi da rage talauci da tinkarar sauyin yanayi da sauransu. Ban da wannan kuma, ma’aikatar aikin noma da raya kauyuka ta kasar sin ta tura masananta fiye da 400 zuwa kasashen Afrika tare da horar da ‘yan Afrika fiye da dubu 10.

  • Yanzu-yanzu: Kotun Daukaka Kara Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Gwamnan Kano Gobe A Abuja
  • Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden

Ban da samar da dabaru na kimiyya da fasaha, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina wasu manyan ababen more rayuwa a wannan fanni. Gwamnatin Sin ta tallafawa Najeriya wajen gina cibiyar raya aikin gona ta gwaji a Abuja kyauta, wannan cibiyar ta fitar da wani nau’in irin shimkafa samfurin Gawal R1, kuma an yi shekaru 5 ana shuka wannan iri a Najeriya, wanda ya samar da karin shinkafa tan miliyan 2, inda manoma fiye da dubu 200 suka ci gajiya. A cikin shekaru 10 da suka gabata, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina cibiyoyin gwaji a fannin aikin noma 24, inda aka gabatar tare da yayata fasahohi fiye da 300 a wuraren, yawan karuwar hatsi da aka samu ya kai kashi 30% zuwa 60%, manoma kimanin miliyan 1 sun ci gajiyar wadannan fasahohi.

ADVERTISEMENT

Yanzu, gwamnatin Sin na kara karfafa hadin gwiwa da kasashen Afrika a wannan fanni, kuma ta gudanar da dandalin hadin kan Sin da Afrika a fannin aikin gona karo na 2 a birnin Sanya na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin daga ran 13 zuwa 15. Dandalin na da zummar habaka hadin kan bangarorin biyu, ta yadda za a kara inganta ayyukan gona a kasashen Afrika, tare da cimma muradun samun ci gaba nan da shekara ta 2030 a wannan bangare a kasashen Afrika.

Ayyukan hadin kai a bangaren aikin noma karkashin shirin hadin kan kasashe masu tasowa da shawarar “ziri daya da hanya daya” sun samarwa kasashe masu tasowa musamman ma kasashen Afrika tallafin manyan ababen more rayuwa a fannin aikin noma da kudade da fasahohi da hatsi da sauransu, matakan da za su taimaka musu wajen samun bunkasuwa da dogara da karfin kansu. Labarin Mojidi da cibiyar gwaji ta fasahohin aikin noma dake Abuja sun zama misali ta fuskar hadin kan Sin da Afrika. Ana sa ran cewa, a cikin shekaru 10 masu zuwa, bangarorin biyu za su samu karin ci gaba a wannan fanni. (Mai zana da rubuta: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Gona
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Next Post
Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.