Wani abu ya sake tashi a yankin Dansadau na karamar hukumar Maru da ke Jihar Zamfara, lamarin da ya ƙara tayar da hankalin jama’ar yankin kan matsalar tsaro.
A ranar Juma’a, bama-bamai biyu sun tashi a kan hanyoyin Dansadau-Malamawa da Malele.
Daya daga cikinsu ya lalata wata mota mai dauke da kayan abinci da ke kan hanyarta na zuwa kasuwar mako-mako ta Dansadau, amma babu wanda ya ji rauni.
Wannan shi ne karo na uku da bam ke tashi a yankin cikin mako É—aya.
A ranar Laraba, bam ya hallaka mutane 12 bayan ya rushe wata gada a kauyen Yar Tasha, inda ya samu wata mota mai É—auke da fasinjoji.
A ranar Lahadi kuma, wata motar kirar bas mai É—aukar mutum 18 ta taka bam, inda direban motsr ya rasa ransa nan take.
Rundunar ‘yansandan jihar, ta alakanta hare-haren da wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda mai suna Lakurawa.
Ana zargin kungiyar da dasa bama-bamai a kan manyan hanyoyi don kai wa matafiya hari.
Jama’a sun bukaci hukumomin tsaro su gaggauta daukar mataki don tabbatar da zaman lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp