Wani matashi mai suna Suleiman Muntari ya ƙone kansa da wuta a Kano ranar Talata, 17 ga watan Yuni, 2025.
Matashin wanda ɗan asalin Jihar Neja ne, amma yana zaune a unguwar Kofar Gadon Kaya a Kano.
- Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya
- An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi
Lamarin ya faru ne a Diga, kusa da hanyar Panshekara.
Shaidu sun ce ya zuba fetur a jikinsa sannan ya kunna wa kansa wuta.
“Ya ce yana so ya je Aljanna,” in ji wani ganau mai suna Saminu Isah wanda ke aiki kusa da wajen.
“Da farko mun ɗauka yana wasa ne, amma kafin wani ya kai ɗauki, ya riga ya kunna wa kansa wuta.”
Wata mazauniyar yankin, Aisha Salisu, ta ce yana matashin yana shaye-shaye.
“Ba ya cikin hayyacinsa. Ana jin warin wani abu mai ƙarfi a jikinsa, kuma yana karkarwa da ihu,” in ji ta.
Mutane sun yi ƙoƙarin taimaka masa.
Wasu sun ja shi zuwa cikin ruwan da ke wata magudanar ruwa a gefen hanya, amma wutar ta riga ta yi masa ƙone sa.
“Abun ya zama kamar fim kuma mai ban tsoro,” in ji wani direban adaidaita sahu mai suna Ibrahim Jafar.
“Ko bayan da suka jefa shi cikin ruwan, wutar ba ta daina ci nan take ba. Fatar jikinsa duk ta ɗaye.”
Hukumomi ba su fitar da wata sanarwa ba tukuna dangane da lamarin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp