ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure

by Salim Sani Shehu
2 years ago
Matashi

Wani Matashi wanda bai jima da kammala karatun digirinsa na farko a Jihar Neja ba, ya yi kokarin mayar da wasu makudan kudade da suka kusan Naira Miliyan 100 da a ka turo masa ta asusun ajiyarsa bisa kuskure.

Yanayin tura kudi zuwa ga wani asusun bisa kuskure, ba bakon abu ba ne a Nijeriya, to amma abin da yake yawan ba wa mutane mamaki shi ne yadda da yawa daga cikin wadanda suke tsintar kansu cikin wannan yanayin, suke mantawa da kuncin rayuwar da ake ciki, su bi tsarin addininsu ko al’adarsu wajen cigiya sabanin wadanda suke amfani da kudin ba tare da tsoron wanda ya halicce su ko kuma za a iya kama su ba.

  • Majalisar Kano Za Ta Karrama Dan Adaidaitan Da Ya Maida Wa Dan Chadi Miliyan 15 Da Ya Tsinta

Abubakar Muhammad, wanda yake taya mahaifinsa kasuwanci a Jihar Neja, ya shiga sahun irin wadannan mutanen na kirki, inda yana zaune kwatsam sai ya ji shigar kudi asusunsa na banki ba tare da sa rai ko kuma kulla ciniki kan kudin ba.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP HAUSA ta zanta da Abubakar kan yanayin yadda al’amarin ya faru.

“Mun kulla huldar kasuwanci da wasu a kan za su turo mun da N310,000, kuma sun tura min kudin a ranar 19 ga watan Oktobar 2023.”

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

Abubakar ya ci gaba da bayyanawa LEADERSHIP HAUSA abinda ya faru a wannan ranar dai ta 19 ga watan Oktoban, in da ya ce, “Bayan kamar minti talatin da turo mun kudin da mukai ciniki a kansu, kawai sai na ga kuma wani sakon na nuna an sa mun Naira Miliyan 84,210,000, wanda kuma ni na san ba mu yi magnarsu ba.”

Abubakar wanda shekarunsa ba su haura Ashirin da Uku ba, ya yi mamaki mutuka da ganin irin wannan makudan kudade da suka kusan kaiwa miliyan 100 da suka shiga asusunsa.

“Ina zaune kawai sai na ga kira daga wadananan mutanen da muka yi cinikin da su, sai suka ce min sun yi kuskure kan kudin da suka turo mun, dan haka suna bukatar na maida musu.”

Ya zuwa yanzu damu ke hada wannan rahoton, Abubakar na magana da wadanda suka turo masa kudin dan ganin ya maida musu hakkinsu, kamar yadda muka tabbatar.

Wannan dai abun da Abubakar ya yi, ya nuna irin kishinsa ga addininsa, da kuma hakura da abunda ba nasa ba ne, halin da ya kamata matasa da al’umma su yi koyi da shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Next Post
Goro

Goron Juma'a

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.