• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure

by Salim Sani Shehu
2 years ago
in Labarai
0
Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani Matashi wanda bai jima da kammala karatun digirinsa na farko a Jihar Neja ba, ya yi kokarin mayar da wasu makudan kudade da suka kusan Naira Miliyan 100 da a ka turo masa ta asusun ajiyarsa bisa kuskure.

Yanayin tura kudi zuwa ga wani asusun bisa kuskure, ba bakon abu ba ne a Nijeriya, to amma abin da yake yawan ba wa mutane mamaki shi ne yadda da yawa daga cikin wadanda suke tsintar kansu cikin wannan yanayin, suke mantawa da kuncin rayuwar da ake ciki, su bi tsarin addininsu ko al’adarsu wajen cigiya sabanin wadanda suke amfani da kudin ba tare da tsoron wanda ya halicce su ko kuma za a iya kama su ba.

  • Majalisar Kano Za Ta Karrama Dan Adaidaitan Da Ya Maida Wa Dan Chadi Miliyan 15 Da Ya Tsinta

Abubakar Muhammad, wanda yake taya mahaifinsa kasuwanci a Jihar Neja, ya shiga sahun irin wadannan mutanen na kirki, inda yana zaune kwatsam sai ya ji shigar kudi asusunsa na banki ba tare da sa rai ko kuma kulla ciniki kan kudin ba.

LEADERSHIP HAUSA ta zanta da Abubakar kan yanayin yadda al’amarin ya faru.

“Mun kulla huldar kasuwanci da wasu a kan za su turo mun da N310,000, kuma sun tura min kudin a ranar 19 ga watan Oktobar 2023.”

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Abubakar ya ci gaba da bayyanawa LEADERSHIP HAUSA abinda ya faru a wannan ranar dai ta 19 ga watan Oktoban, in da ya ce, “Bayan kamar minti talatin da turo mun kudin da mukai ciniki a kansu, kawai sai na ga kuma wani sakon na nuna an sa mun Naira Miliyan 84,210,000, wanda kuma ni na san ba mu yi magnarsu ba.”

Abubakar wanda shekarunsa ba su haura Ashirin da Uku ba, ya yi mamaki mutuka da ganin irin wannan makudan kudade da suka kusan kaiwa miliyan 100 da suka shiga asusunsa.

“Ina zaune kawai sai na ga kira daga wadananan mutanen da muka yi cinikin da su, sai suka ce min sun yi kuskure kan kudin da suka turo mun, dan haka suna bukatar na maida musu.”

Ya zuwa yanzu damu ke hada wannan rahoton, Abubakar na magana da wadanda suka turo masa kudin dan ganin ya maida musu hakkinsu, kamar yadda muka tabbatar.

Wannan dai abun da Abubakar ya yi, ya nuna irin kishinsa ga addininsa, da kuma hakura da abunda ba nasa ba ne, halin da ya kamata matasa da al’umma su yi koyi da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Matashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina

Next Post

Goron Juma’a

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

3 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

4 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

4 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

5 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

7 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

8 hours ago
Next Post
Goro

Goron Juma'a

LABARAI MASU NASABA

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.