ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure

by Salim Sani Shehu
3 years ago
Matashi

Wani Matashi wanda bai jima da kammala karatun digirinsa na farko a Jihar Neja ba, ya yi kokarin mayar da wasu makudan kudade da suka kusan Naira Miliyan 100 da a ka turo masa ta asusun ajiyarsa bisa kuskure.

Yanayin tura kudi zuwa ga wani asusun bisa kuskure, ba bakon abu ba ne a Nijeriya, to amma abin da yake yawan ba wa mutane mamaki shi ne yadda da yawa daga cikin wadanda suke tsintar kansu cikin wannan yanayin, suke mantawa da kuncin rayuwar da ake ciki, su bi tsarin addininsu ko al’adarsu wajen cigiya sabanin wadanda suke amfani da kudin ba tare da tsoron wanda ya halicce su ko kuma za a iya kama su ba.

  • Majalisar Kano Za Ta Karrama Dan Adaidaitan Da Ya Maida Wa Dan Chadi Miliyan 15 Da Ya Tsinta

Abubakar Muhammad, wanda yake taya mahaifinsa kasuwanci a Jihar Neja, ya shiga sahun irin wadannan mutanen na kirki, inda yana zaune kwatsam sai ya ji shigar kudi asusunsa na banki ba tare da sa rai ko kuma kulla ciniki kan kudin ba.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP HAUSA ta zanta da Abubakar kan yanayin yadda al’amarin ya faru.

“Mun kulla huldar kasuwanci da wasu a kan za su turo mun da N310,000, kuma sun tura min kudin a ranar 19 ga watan Oktobar 2023.”

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Abubakar ya ci gaba da bayyanawa LEADERSHIP HAUSA abinda ya faru a wannan ranar dai ta 19 ga watan Oktoban, in da ya ce, “Bayan kamar minti talatin da turo mun kudin da mukai ciniki a kansu, kawai sai na ga kuma wani sakon na nuna an sa mun Naira Miliyan 84,210,000, wanda kuma ni na san ba mu yi magnarsu ba.”

Abubakar wanda shekarunsa ba su haura Ashirin da Uku ba, ya yi mamaki mutuka da ganin irin wannan makudan kudade da suka kusan kaiwa miliyan 100 da suka shiga asusunsa.

“Ina zaune kawai sai na ga kira daga wadananan mutanen da muka yi cinikin da su, sai suka ce min sun yi kuskure kan kudin da suka turo mun, dan haka suna bukatar na maida musu.”

Ya zuwa yanzu damu ke hada wannan rahoton, Abubakar na magana da wadanda suka turo masa kudin dan ganin ya maida musu hakkinsu, kamar yadda muka tabbatar.

Wannan dai abun da Abubakar ya yi, ya nuna irin kishinsa ga addininsa, da kuma hakura da abunda ba nasa ba ne, halin da ya kamata matasa da al’umma su yi koyi da shi.

Matashi
Salim Sani Shehu
+ postsBio
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Adeleke Ya Lashe Zaɓen Osun Da Ƙuri’u 511,067
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Goro

Goron Juma'a

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.