• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Mutum Ya Kashe Mahaifiyarsa Kan Naira 10,000

by Khalid Idris Doya
2 years ago

Wani mutum da aka bayyana sunansa da Osaro Owate, ya shiga hannun hukumar ‘yansandan jihar Ribas bisa zargin kashe mahaifiyarsa a kauyen Alesa da ke karamar hukumar Eleme kan rashin jituwar da ta shiga tsakaninsu kan naira dubu goma (N10,000) kacal.

Wanda ake zargin, ya yi ikirarin cewa ya na fama da matsalar gaulanci ko tsatstsauran ra’ayin addini na tsawon sama da shekara 30, ya amsa da bakinsa kan cewa ya kashe mamar tasa da fartanya ne.

  • Amurka Ba Za Ta Cimma Yunkurin Taron Dangi Bisa Fakewa Da Batun Taiwan Ba

Da yake magana ta cikin wani faifayin bidiyon da ya yadu sosai a Soshal Midiya, Owate ya ce, ya bukaci naira dubu ashirin (N20,000) a wajen marigayiyar mamar tasa domin ya sayi kayan sawa da zan yi adon zuwa wajen bisne wata gawa, amma sai ta ba shi naira 10 kacal, kuma hakan ya kasa masa matuka

Wanda ake zargin ya ce, “Jiya (Ranar Juma’a), na fada mata zuwa safiyar Asabar ta ciro kudin da za ta bani da zan sanyi kayan sanyawa domin halartar bikin biso. Da safiyar yau din kafin na tashi sai ya zama ita ta kama shirye-shiryen fita daga gida domin ta je ta halarci bikin biso.

“Na tambayeta maganar kudin da na bukata daga wajenta na ce ko dai ba ta son na halarci wajen bison ne kuma. Sai ta ce to bari za ta ciro min kudin.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

“Ta tafi ta je ta ciro N20,000 da muka hadu sai ta dauko N10,000 kacal ta ba ni. Na sha mamakin a inane zan samu kayan dubu goma na saya.

“Da na kama binta, sai ta fara musguna min da zagina wai sa’o’ina su na aiki su na sana’a don meye ni nake zaman banza bana sana’ar komai. Na tunatar da ita cewa ina fama da matsalar da ke damuna ta yaya zan je na nemi aiki alhalin ina da matsala.?

“Amma duk da hakan ta cigaba da surfamin fada kawai sai na bugeta da fartanya. Tana kicin domin dafa abinci ne lokacin da na buga mata fartanya. Da na fusata matuka, kawai sai na gama da ita. Idan ni ma rayuwata za ta kawo karshe don na yi hakan ba damuwa na mutun kawai na shirya ma hakan. Ina fama da matsalar gaulanci sama da shekara 30. Kamar yadda kuke kallona yanzu ina son na mutum.”

Har zuwa lokacin hada wannan rahoton rundunar ‘yansandan jihar Ribas ba ta fitar da wani bayani a kai ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri
Labarai

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Cafke Mutane 218 Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi Masu Nauyin Kilo 5,610 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.