• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Rahoto Ya Fallasa Hanyoyin Da Doka Ta Tanada Don Kare Masu Aikata Fyaɗe A Afirka

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
Rahoto

Wani rahoto da wata kungiya mai zaman kanta ta kasa da kasa Ekuality Now ta fitar, ya ce ma’anar fyade a kasashen Afirka 25 ya ba da dama ga masu aikata laifuka su tafiyarsu ba tare da an tuhume su da wani laifi ba.

Sakamakon binciken wani bangare ne na wani bincike mai shafuka 46 da ya bankado gibi a fannin dokoki da aiwatarwa da kuma samun adalci ga wadanda aka yi wa fyade a kasashen Afirka 47.

  • An Yi Wa Matashi Hukuncin Daurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Yarinya Fyade A Kebbi
  • Yara Mata Miliyan 370 Ke Fuskantar Cin Zarafi Da Fyade A Duniya –UNICEF

Rahoton ya ce a duniya kashi 35 cikin 100 na mata sun fuskanci cin zarafi na jiki ko na lalata, kuma kusan kashi 33 cikin 100 na mata a Afirka sun fuskanci cin zarafi a rayuwarsu.

Rahoton ya ce an samu karuwar yawan cin zarafin mata a lokacin tashe-tashen hankula a kasashen Habasha da Sudan da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, in ji rahoton, wanda ya kara da cewa a wadannan kasashe, ana amfani da fade a matsayin makamin yaki wajen bata wa al’umma rai.

Sally Ncube, wakiliyar yanki ce ta Ekuality Now a kudancin Afirka a Yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Ta fadawa Muryar Amurka ta wata manhajar aika sako daga kasar Zimbabwe cewa takaitattun ma’anar fyade da aka dade suna karfafa rashin hukunta masu aikata laifuka a kasashe da dama.

Ta ce “Misali, fyade da aka aikata a cikin kusanci da abokin tarayya, ana mayar da wadannan laifuka zuwa kananan laifuka, tare da kananan hukunce-hukunce da ke haifar da wani sako mai rudani game da cikakken hakkin kowane mutum na cin gashin kansa.”

Rahoton ya bayyana sunayen kasashe 25 na Afirka, inda ma’anar fyade da doka ta tanada ya yi kadan. Sun hada da Kamaru da Sudan ta Kudu da Chadi da Ekuatorial Guinea da Gabon da Gambia da Mozambikue da kuma Malawi.

Zione Lapani ita ce mai daidaita sashin tallafawa wadanda abin ya shafa a ofishin ‘yan sanda na Blantyre a Malawi.

Ta fadawa Muryar Amurka wani lamari da wata matar aure ta kai karar ‘yan sanda bayan da mijin ya yi lalata da ita.

Lapani ta ce ba su bude wata kara ba bayan tattaunawa da ma’auratan da suka tabbatar da cewa, mutumin ya tilasta wa matarsa yin lalata da ita na tsawon lokaci saboda wasu batutuwan iyali.

Wani rahoto na Ekuality Now game da gibi a cikin dokokin iyali da aka fitar a farkon wannan shekarar, ya gano cewa dokar al’ada ta Malawi tana daukar amincewar har abada don yin jima’i a cikin aure, kuma mace za ta iya hana mijinta yin jima’i ne kawai idan ba ta da lafiya ko kuma ta hanyar rabuwa bisa doka.

Sai dai kuma rahoton ya ce kasar Rwanda ta dauki muhimman matakai domin inganta binciken wadanda zalunta, tare a hukunta laifukan cin zarafin mata.

Har ila yau, ta ce Senegal ta dauki irin wannan matakin ta hanyar kafa “Cibiyoyin doka” da ke ba da taimakon shari’a da zamantakewa.

Kuma a Malawi kotuna sun fara yanke hukunci mai tsauri ga wadanda aka samu da laifin fyade.

Misali, a shekara ta 2021, wata babbar kotu a kudancin Malawi ta yanke wa wani mutum dan shekara 33 hukuncin daurin shekaru 40 a gidan yari, saboda ya yi wa yarinya ‘yar shekara tara fyade.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 
Labarai

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba
Labarai

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Next Post
Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.