ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara Mata Miliyan 370 Ke Fuskantar Cin Zarafi Da Fyade A Duniya –UNICEF

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zarafi

Wani rahoto da asusun na UNICEF ya fitar, ya bayyana cewa daya daga cikin kowadanne yara mata 8 a duniya suna fuskantar hadarin cin zarafi da fyade. Daya daga cikin matan 5 kuma suna fuskantar irin wannan barazana ta hanyar kafofin sada zumunta na zamani, wanda adadinsu ya kai miliyan 650.

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, UINCEF ya ce, yara mata miliyan 370 ke fuskantar cin zarafi ko kuma fyade kafin su cika shekaru 18 da haihuwa a fadin duniya.

  • Hadin Gurasa Na Zamani
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron AIPPI Na Duniya Na 2024

Rahoton na UNICEF ya kara da cewa adadin cin zarafin yara mata na ci gaba da fadada a sassan duniya, inda yara mata miliyan 79 wanda ya yi daidai da kaso 22 ke fuskantar cin zarafi a kasashen nahiyar Afirka da ke Kudancin Sahara, kafin cikar haihuwarsu shekaru 18.

ADVERTISEMENT

Sai kuma kasashen da ke Gabashi da kuma Gabas maso Kudancin Asiya, da suke da kaso 8 da adadinsu ya kai yara mata miliyan 75 ne ke fuskantar cin zarafin.

Yara mata miliyan 73 a tsakiyar Asiya da kuma Kudancinta ke fuskantar irin wannan cin zarafi, kafin cikarsu shekaru 18 da haihuwa, inda kason ya kai 9.

LABARAI MASU NASABA

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

Tarayyar Turai da kuma Arewacin Amurka na da kaso 14 da adadin su ya kai miliyan 68 na yara mata da ke fuskantar irin wannan kalubale, a cewar UNICEF.

Yara mata miliyan 45 ne a yankin Latin Amurka da Caribbean, sai kuma yara mata miliyan 29 a Arewacin Afirka da Yammacin Asiya, da kuma yara mata miliyan 6 a yankin Oceania, inda suke da kaso 18, 15 da kuma kaso 34 na yara mata da ke fuskantar cin zarafi da kuma fyade.

Fatima Usman, daya ce daga cikin iyaye wacce ‘yarta ta taba fuskantar irin wannan cin zarafi a Nijeriya. Ta ce ta ran ta yana kuna sosai a duk lokacin da ta tuna da wannan al’amarin

Dakta Hauwa Babura, daya ce daga cikin mata masu fafutakar kare ‘yancin yara mata a Nijeriya, ta kuma jaddada kididdigar rahoton da UNICEF, ta fitar.

A hirarsa da Muryar Amurka, Isa Sanusi, wanda shi ne Babban Daraktan Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta Amnesty International a Nijeriya, ya ce, yara ma na fuskantar yawaitar fyade da cin zarafi a yankunan da ke fuskantar tashe-tashen hankula a Nijeriya.

Masana na ganin daukar matakai masu tsauri ne kadai hanyar da za ta kawo karshen cin zarafin yara a duniya.

Zarafi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei
Kasashen Ketare

Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

July 1, 2026
Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Yadda Muka Dakatar Da Yunkurin Tsige Ganduje Daga Shugabancin APC - Kungiyar Arewa Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.