ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara Mata Miliyan 370 Ke Fuskantar Cin Zarafi Da Fyade A Duniya –UNICEF

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zarafi

Wani rahoto da asusun na UNICEF ya fitar, ya bayyana cewa daya daga cikin kowadanne yara mata 8 a duniya suna fuskantar hadarin cin zarafi da fyade. Daya daga cikin matan 5 kuma suna fuskantar irin wannan barazana ta hanyar kafofin sada zumunta na zamani, wanda adadinsu ya kai miliyan 650.

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, UINCEF ya ce, yara mata miliyan 370 ke fuskantar cin zarafi ko kuma fyade kafin su cika shekaru 18 da haihuwa a fadin duniya.

  • Hadin Gurasa Na Zamani
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron AIPPI Na Duniya Na 2024

Rahoton na UNICEF ya kara da cewa adadin cin zarafin yara mata na ci gaba da fadada a sassan duniya, inda yara mata miliyan 79 wanda ya yi daidai da kaso 22 ke fuskantar cin zarafi a kasashen nahiyar Afirka da ke Kudancin Sahara, kafin cikar haihuwarsu shekaru 18.

ADVERTISEMENT

Sai kuma kasashen da ke Gabashi da kuma Gabas maso Kudancin Asiya, da suke da kaso 8 da adadinsu ya kai yara mata miliyan 75 ne ke fuskantar cin zarafin.

Yara mata miliyan 73 a tsakiyar Asiya da kuma Kudancinta ke fuskantar irin wannan cin zarafi, kafin cikarsu shekaru 18 da haihuwa, inda kason ya kai 9.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Tarayyar Turai da kuma Arewacin Amurka na da kaso 14 da adadin su ya kai miliyan 68 na yara mata da ke fuskantar irin wannan kalubale, a cewar UNICEF.

Yara mata miliyan 45 ne a yankin Latin Amurka da Caribbean, sai kuma yara mata miliyan 29 a Arewacin Afirka da Yammacin Asiya, da kuma yara mata miliyan 6 a yankin Oceania, inda suke da kaso 18, 15 da kuma kaso 34 na yara mata da ke fuskantar cin zarafi da kuma fyade.

Fatima Usman, daya ce daga cikin iyaye wacce ‘yarta ta taba fuskantar irin wannan cin zarafi a Nijeriya. Ta ce ta ran ta yana kuna sosai a duk lokacin da ta tuna da wannan al’amarin

Dakta Hauwa Babura, daya ce daga cikin mata masu fafutakar kare ‘yancin yara mata a Nijeriya, ta kuma jaddada kididdigar rahoton da UNICEF, ta fitar.

A hirarsa da Muryar Amurka, Isa Sanusi, wanda shi ne Babban Daraktan Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta Amnesty International a Nijeriya, ya ce, yara ma na fuskantar yawaitar fyade da cin zarafi a yankunan da ke fuskantar tashe-tashen hankula a Nijeriya.

Masana na ganin daukar matakai masu tsauri ne kadai hanyar da za ta kawo karshen cin zarafin yara a duniya.

Zarafi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

MASU ALAKA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
Kasashen Ketare

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
Kasashen Ketare

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Yadda Muka Dakatar Da Yunkurin Tsige Ganduje Daga Shugabancin APC - Kungiyar Arewa Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.