ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Rahoto Ya Fallasa Hanyoyin Da Doka Ta Tanada Don Kare Masu Aikata Fyaɗe A Afirka

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Rahoto

Wani rahoto da wata kungiya mai zaman kanta ta kasa da kasa Ekuality Now ta fitar, ya ce ma’anar fyade a kasashen Afirka 25 ya ba da dama ga masu aikata laifuka su tafiyarsu ba tare da an tuhume su da wani laifi ba.

Sakamakon binciken wani bangare ne na wani bincike mai shafuka 46 da ya bankado gibi a fannin dokoki da aiwatarwa da kuma samun adalci ga wadanda aka yi wa fyade a kasashen Afirka 47.

  • An Yi Wa Matashi Hukuncin Daurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Yarinya Fyade A Kebbi
  • Yara Mata Miliyan 370 Ke Fuskantar Cin Zarafi Da Fyade A Duniya –UNICEF

Rahoton ya ce a duniya kashi 35 cikin 100 na mata sun fuskanci cin zarafi na jiki ko na lalata, kuma kusan kashi 33 cikin 100 na mata a Afirka sun fuskanci cin zarafi a rayuwarsu.

ADVERTISEMENT

Rahoton ya ce an samu karuwar yawan cin zarafin mata a lokacin tashe-tashen hankula a kasashen Habasha da Sudan da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, in ji rahoton, wanda ya kara da cewa a wadannan kasashe, ana amfani da fade a matsayin makamin yaki wajen bata wa al’umma rai.

Sally Ncube, wakiliyar yanki ce ta Ekuality Now a kudancin Afirka a Yanzu.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ta fadawa Muryar Amurka ta wata manhajar aika sako daga kasar Zimbabwe cewa takaitattun ma’anar fyade da aka dade suna karfafa rashin hukunta masu aikata laifuka a kasashe da dama.

Ta ce “Misali, fyade da aka aikata a cikin kusanci da abokin tarayya, ana mayar da wadannan laifuka zuwa kananan laifuka, tare da kananan hukunce-hukunce da ke haifar da wani sako mai rudani game da cikakken hakkin kowane mutum na cin gashin kansa.”

Rahoton ya bayyana sunayen kasashe 25 na Afirka, inda ma’anar fyade da doka ta tanada ya yi kadan. Sun hada da Kamaru da Sudan ta Kudu da Chadi da Ekuatorial Guinea da Gabon da Gambia da Mozambikue da kuma Malawi.

Zione Lapani ita ce mai daidaita sashin tallafawa wadanda abin ya shafa a ofishin ‘yan sanda na Blantyre a Malawi.

Ta fadawa Muryar Amurka wani lamari da wata matar aure ta kai karar ‘yan sanda bayan da mijin ya yi lalata da ita.

Lapani ta ce ba su bude wata kara ba bayan tattaunawa da ma’auratan da suka tabbatar da cewa, mutumin ya tilasta wa matarsa yin lalata da ita na tsawon lokaci saboda wasu batutuwan iyali.

Wani rahoto na Ekuality Now game da gibi a cikin dokokin iyali da aka fitar a farkon wannan shekarar, ya gano cewa dokar al’ada ta Malawi tana daukar amincewar har abada don yin jima’i a cikin aure, kuma mace za ta iya hana mijinta yin jima’i ne kawai idan ba ta da lafiya ko kuma ta hanyar rabuwa bisa doka.

Sai dai kuma rahoton ya ce kasar Rwanda ta dauki muhimman matakai domin inganta binciken wadanda zalunta, tare a hukunta laifukan cin zarafin mata.

Har ila yau, ta ce Senegal ta dauki irin wannan matakin ta hanyar kafa “Cibiyoyin doka” da ke ba da taimakon shari’a da zamantakewa.

Kuma a Malawi kotuna sun fara yanke hukunci mai tsauri ga wadanda aka samu da laifin fyade.

Misali, a shekara ta 2021, wata babbar kotu a kudancin Malawi ta yanke wa wani mutum dan shekara 33 hukuncin daurin shekaru 40 a gidan yari, saboda ya yi wa yarinya ‘yar shekara tara fyade.

Rahoto
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.