ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Rahoto Ya Fallasa Hanyoyin Da Doka Ta Tanada Don Kare Masu Aikata Fyaɗe A Afirka

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Rahoto

Wani rahoto da wata kungiya mai zaman kanta ta kasa da kasa Ekuality Now ta fitar, ya ce ma’anar fyade a kasashen Afirka 25 ya ba da dama ga masu aikata laifuka su tafiyarsu ba tare da an tuhume su da wani laifi ba.

Sakamakon binciken wani bangare ne na wani bincike mai shafuka 46 da ya bankado gibi a fannin dokoki da aiwatarwa da kuma samun adalci ga wadanda aka yi wa fyade a kasashen Afirka 47.

  • An Yi Wa Matashi Hukuncin Daurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Yarinya Fyade A Kebbi
  • Yara Mata Miliyan 370 Ke Fuskantar Cin Zarafi Da Fyade A Duniya –UNICEF

Rahoton ya ce a duniya kashi 35 cikin 100 na mata sun fuskanci cin zarafi na jiki ko na lalata, kuma kusan kashi 33 cikin 100 na mata a Afirka sun fuskanci cin zarafi a rayuwarsu.

ADVERTISEMENT

Rahoton ya ce an samu karuwar yawan cin zarafin mata a lokacin tashe-tashen hankula a kasashen Habasha da Sudan da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, in ji rahoton, wanda ya kara da cewa a wadannan kasashe, ana amfani da fade a matsayin makamin yaki wajen bata wa al’umma rai.

Sally Ncube, wakiliyar yanki ce ta Ekuality Now a kudancin Afirka a Yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ta fadawa Muryar Amurka ta wata manhajar aika sako daga kasar Zimbabwe cewa takaitattun ma’anar fyade da aka dade suna karfafa rashin hukunta masu aikata laifuka a kasashe da dama.

Ta ce “Misali, fyade da aka aikata a cikin kusanci da abokin tarayya, ana mayar da wadannan laifuka zuwa kananan laifuka, tare da kananan hukunce-hukunce da ke haifar da wani sako mai rudani game da cikakken hakkin kowane mutum na cin gashin kansa.”

Rahoton ya bayyana sunayen kasashe 25 na Afirka, inda ma’anar fyade da doka ta tanada ya yi kadan. Sun hada da Kamaru da Sudan ta Kudu da Chadi da Ekuatorial Guinea da Gabon da Gambia da Mozambikue da kuma Malawi.

Zione Lapani ita ce mai daidaita sashin tallafawa wadanda abin ya shafa a ofishin ‘yan sanda na Blantyre a Malawi.

Ta fadawa Muryar Amurka wani lamari da wata matar aure ta kai karar ‘yan sanda bayan da mijin ya yi lalata da ita.

Lapani ta ce ba su bude wata kara ba bayan tattaunawa da ma’auratan da suka tabbatar da cewa, mutumin ya tilasta wa matarsa yin lalata da ita na tsawon lokaci saboda wasu batutuwan iyali.

Wani rahoto na Ekuality Now game da gibi a cikin dokokin iyali da aka fitar a farkon wannan shekarar, ya gano cewa dokar al’ada ta Malawi tana daukar amincewar har abada don yin jima’i a cikin aure, kuma mace za ta iya hana mijinta yin jima’i ne kawai idan ba ta da lafiya ko kuma ta hanyar rabuwa bisa doka.

Sai dai kuma rahoton ya ce kasar Rwanda ta dauki muhimman matakai domin inganta binciken wadanda zalunta, tare a hukunta laifukan cin zarafin mata.

Har ila yau, ta ce Senegal ta dauki irin wannan matakin ta hanyar kafa “Cibiyoyin doka” da ke ba da taimakon shari’a da zamantakewa.

Kuma a Malawi kotuna sun fara yanke hukunci mai tsauri ga wadanda aka samu da laifin fyade.

Misali, a shekara ta 2021, wata babbar kotu a kudancin Malawi ta yanke wa wani mutum dan shekara 33 hukuncin daurin shekaru 40 a gidan yari, saboda ya yi wa yarinya ‘yar shekara tara fyade.

Rahoto
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.