• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata, yayin da Sinawa suke murnar bikin sabuwar shekara ta gargajiya, an ji wani albishir daga Najeriya, wato an kaddamar da tashar jirgin ruwa ta Lekki a jihar Lagos, a ranar 23 ga watan Janairun bana.

Na tuna da lokacin da nake aiki a Najeriya a shekarar 2008, ana kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na Lekki, wanda kamfanonin kasar Sin suka zuba jari a ciki.

  • Shugaban Najeriya Ya Yi Maraba Da Isowar Jirgin Ruwan Farko A Tashar Jiragen Ruwa Da Ke Ruwa Mai Zurfi Ta Lekki

A lokacin, wasu abokaina Sinawa sun gaya mana cewa, nan gaba za a gina wata babbar tashar jirgin ruwa a kudancin yankin ciniki mai ‘yancin, wadda za ta taimakawa raya masana’antu da aikin fitar da kayayyaki zuwa ketare a cikin yankin.

To, ga shi, yanzu an riga an cimma burin da aka sanya. Ta haka za mu iya ganin yadda kasar Najeriya take kokarin neman samun hakikanin ci gaba, duk da matsalolin da take fuskanta a fannonin tattalin arziki da tsaro, cikin wadannan shekarun da suka gabata.

Wannan sabuwar tashar jirgin ruwa dake Lekki ta burge ni a fannoni daban daban.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Da farko, wata ingantacciyar tasha ce da ake samun ruwa mai zurfi. Da ma na taba ganin wasu manyan jiragen ruwa masu daukar kaya, da suka tsaya a tashar jirgin ruwa dake Apapa da Tin Can Island, duk a jihar Lagos. Sai dai girman jirgin ruwan da tashar Lekki za ta iya dauka, ya ninka na wadancan jiragen ruwa har sau 4, wanda ya wuce na jirgin ruwa mafi girma da ake samu yanzu a duniyarmu. Ban da wannan kuma, wannan tashar jirgin ruwa za ta iya karbar kwantaina miliyan 1.2 a duk shekara, wanda yake kan gaba cikin dukkan tashoshin jirgin ruwa dake yammacin Afirka.

Na biyu, wannan sabuwar tasha za ta haifar da dimbin alfanu. A cewar gwamnan jihar Lagos ta Najeriya, Babajide Sanwo-Olu, wannan sabuwar tasha za ta sanya Lagos zama cibiyar jigilar kayayyaki ta hanyar teku dake tsakiya da yammacin Afirka, da samarwa Najeriya da guraben aikin yi da yawansu ya kai kusan dubu 200, inda ta haka za a samar da kyakkyawar damar raya tattalin arzikin kasar.

Sa’an nan na uku shi ne, dukkan ayyukan da suka shafi zuba jari, da ginawa, da ba da kulawa, masu alaka da wannan tasha, ana gudanar da su ne ta hanyar hadin gwiwar bangarorin kasashe daban daban. Inda kamfanonin kasar Sin, da na kasar Singapore, da hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya, da gwamnatin jihar Lagos suka zuba jari tare, sa’an nan wani kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin gina tasha, daga baya kuma, aka ba wani kamfanin kasar Faransa ragamar kulawa da gudanar da harkokin tashar. Wannan tsarin da ake bi ya nuna manufar sanya kowa ya shiga a dama da shi, da aiwatar da aiki ba tare da rufa-rufa ba, da ginawa gami da cin moriyar tashar tare.

Ban da wannan kuma, a matsayi na na wani Basine, ni ma ina alfahari da wannan sabuwar tashar jirgin ruwa.

Saboda wani kamfanin kasar Sin ya taka muhimmiyar rawa wajen aikin gina wannan tasha. Inda a cikin dalar Amurka biliyan 1.044 da aka zuba cikin tashar, kudin da wannan kamfanin kasar Sin ya zuba ya kai dala miliyan 221. Haka kuma, an fara aikin gina tashar a watan Yunin shekarar 2020, da kammala aikin a watan Oktoban shekarar 2022, daga baya an kaddamar da ita a farkon shekarar 2023, wanda ya zama watanni 2 kafin lokacin da aka tsara. Da ma mutane da yawa sun damu kan cewar watakila ba za a iya kammala aikin gini cikin lokaci ba, sakamakon annobar COVID-19 dake yaduwa a sassa daban daban. Amma wannan kamfanin kasar Sin da ya dauki nauyin gina tashar ya cika alkawarin da ya dauka, abun da ya nuna yadda yake da sahihanci da kwarewar aiki.

Ban da haka, ya kamata mu lura da cewa, dalilin da ya sa wannan kamfanin Sin zuba jari, da samar da fasahohi, da tura ma’aikatansa zuwa wajen gina tashar, shi ne domin shawarar hadin gwiwa ta “Ziri Daya da Hanya Daya” (B&R) da kasar Sin ta gabatar, gami da tunani na cin moriya tare gami da samun ci gaba tare da ya zama tubalin shawarar.

Wannan tunani ya tabbatar da aikace-aikacen kasar Sin, inda maimakon ta zama wata “shugaba” ko kuma “mai ba da sadaka” ga kasashen Afirka, take kokarin shiga aikin raya kasashen bisa matsayinta na wata abokiya dake son gudanar da takamaiman ayyukan hadin gwiwa. Kana yayin da ake gudanar da hadin gwiwar, kasar Sin ta tsaya kan manufar tattaunawa, da cin moriya tare, da gudanar da aiki tare, da girmama ka’idojin kasuwanci da na kasa da kasa, da lura da moriyar bangarori daban daban da damuwarsu, ta yadda take samarwa kasashen Afirka da hakikanin ci gaba.

Idan ana son tabbatar da sahihancin Sinawa yayin da ake hadin gwiwa da su, to, wannan sabuwar tashar jirgin ruwa dake Lekki shaida ce. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

Next Post

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Related

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

3 hours ago
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

5 hours ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

5 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

7 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

8 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

9 hours ago
Next Post
Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.