• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata, yayin da Sinawa suke murnar bikin sabuwar shekara ta gargajiya, an ji wani albishir daga Najeriya, wato an kaddamar da tashar jirgin ruwa ta Lekki a jihar Lagos, a ranar 23 ga watan Janairun bana.

Na tuna da lokacin da nake aiki a Najeriya a shekarar 2008, ana kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na Lekki, wanda kamfanonin kasar Sin suka zuba jari a ciki.

  • Shugaban Najeriya Ya Yi Maraba Da Isowar Jirgin Ruwan Farko A Tashar Jiragen Ruwa Da Ke Ruwa Mai Zurfi Ta Lekki

A lokacin, wasu abokaina Sinawa sun gaya mana cewa, nan gaba za a gina wata babbar tashar jirgin ruwa a kudancin yankin ciniki mai ‘yancin, wadda za ta taimakawa raya masana’antu da aikin fitar da kayayyaki zuwa ketare a cikin yankin.

To, ga shi, yanzu an riga an cimma burin da aka sanya. Ta haka za mu iya ganin yadda kasar Najeriya take kokarin neman samun hakikanin ci gaba, duk da matsalolin da take fuskanta a fannonin tattalin arziki da tsaro, cikin wadannan shekarun da suka gabata.

Wannan sabuwar tashar jirgin ruwa dake Lekki ta burge ni a fannoni daban daban.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Da farko, wata ingantacciyar tasha ce da ake samun ruwa mai zurfi. Da ma na taba ganin wasu manyan jiragen ruwa masu daukar kaya, da suka tsaya a tashar jirgin ruwa dake Apapa da Tin Can Island, duk a jihar Lagos. Sai dai girman jirgin ruwan da tashar Lekki za ta iya dauka, ya ninka na wadancan jiragen ruwa har sau 4, wanda ya wuce na jirgin ruwa mafi girma da ake samu yanzu a duniyarmu. Ban da wannan kuma, wannan tashar jirgin ruwa za ta iya karbar kwantaina miliyan 1.2 a duk shekara, wanda yake kan gaba cikin dukkan tashoshin jirgin ruwa dake yammacin Afirka.

Na biyu, wannan sabuwar tasha za ta haifar da dimbin alfanu. A cewar gwamnan jihar Lagos ta Najeriya, Babajide Sanwo-Olu, wannan sabuwar tasha za ta sanya Lagos zama cibiyar jigilar kayayyaki ta hanyar teku dake tsakiya da yammacin Afirka, da samarwa Najeriya da guraben aikin yi da yawansu ya kai kusan dubu 200, inda ta haka za a samar da kyakkyawar damar raya tattalin arzikin kasar.

Sa’an nan na uku shi ne, dukkan ayyukan da suka shafi zuba jari, da ginawa, da ba da kulawa, masu alaka da wannan tasha, ana gudanar da su ne ta hanyar hadin gwiwar bangarorin kasashe daban daban. Inda kamfanonin kasar Sin, da na kasar Singapore, da hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya, da gwamnatin jihar Lagos suka zuba jari tare, sa’an nan wani kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin gina tasha, daga baya kuma, aka ba wani kamfanin kasar Faransa ragamar kulawa da gudanar da harkokin tashar. Wannan tsarin da ake bi ya nuna manufar sanya kowa ya shiga a dama da shi, da aiwatar da aiki ba tare da rufa-rufa ba, da ginawa gami da cin moriyar tashar tare.

Ban da wannan kuma, a matsayi na na wani Basine, ni ma ina alfahari da wannan sabuwar tashar jirgin ruwa.

Saboda wani kamfanin kasar Sin ya taka muhimmiyar rawa wajen aikin gina wannan tasha. Inda a cikin dalar Amurka biliyan 1.044 da aka zuba cikin tashar, kudin da wannan kamfanin kasar Sin ya zuba ya kai dala miliyan 221. Haka kuma, an fara aikin gina tashar a watan Yunin shekarar 2020, da kammala aikin a watan Oktoban shekarar 2022, daga baya an kaddamar da ita a farkon shekarar 2023, wanda ya zama watanni 2 kafin lokacin da aka tsara. Da ma mutane da yawa sun damu kan cewar watakila ba za a iya kammala aikin gini cikin lokaci ba, sakamakon annobar COVID-19 dake yaduwa a sassa daban daban. Amma wannan kamfanin kasar Sin da ya dauki nauyin gina tashar ya cika alkawarin da ya dauka, abun da ya nuna yadda yake da sahihanci da kwarewar aiki.

Ban da haka, ya kamata mu lura da cewa, dalilin da ya sa wannan kamfanin Sin zuba jari, da samar da fasahohi, da tura ma’aikatansa zuwa wajen gina tashar, shi ne domin shawarar hadin gwiwa ta “Ziri Daya da Hanya Daya” (B&R) da kasar Sin ta gabatar, gami da tunani na cin moriya tare gami da samun ci gaba tare da ya zama tubalin shawarar.

Wannan tunani ya tabbatar da aikace-aikacen kasar Sin, inda maimakon ta zama wata “shugaba” ko kuma “mai ba da sadaka” ga kasashen Afirka, take kokarin shiga aikin raya kasashen bisa matsayinta na wata abokiya dake son gudanar da takamaiman ayyukan hadin gwiwa. Kana yayin da ake gudanar da hadin gwiwar, kasar Sin ta tsaya kan manufar tattaunawa, da cin moriya tare, da gudanar da aiki tare, da girmama ka’idojin kasuwanci da na kasa da kasa, da lura da moriyar bangarori daban daban da damuwarsu, ta yadda take samarwa kasashen Afirka da hakikanin ci gaba.

Idan ana son tabbatar da sahihancin Sinawa yayin da ake hadin gwiwa da su, to, wannan sabuwar tashar jirgin ruwa dake Lekki shaida ce. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

Next Post

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Related

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

8 hours ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

9 hours ago
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya
Daga Birnin Sin

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

10 hours ago
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya
Daga Birnin Sin

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

11 hours ago
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

12 hours ago
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Spaniya Da Na Malaysia Da Na Singapore
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Spaniya Da Na Malaysia Da Na Singapore

12 hours ago
Next Post
Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.