• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Takarda Ta Nuna Burin Kasar Sin A Fannin Hulda Da Sauran Kasashe

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wannan Takarda Ta Nuna Burin Kasar Sin A Fannin Hulda Da Sauran Kasashe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da nake karanta bayanan da aka rubuta a Facebook, na ga yawancin bayanai masu alaka da huldar dake tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin sun nuna wani yanayi mai yakini da yabo. Sai dai ra’ayi riga, ba za a rasa wani mutum mai dauke da wani ra’ayi na daban ba. Misali, a ganin wasu mutane, wai “Sinawa sun yi kama da Turawa, sun je nahiyar Afirka don kwashe albarkatu maimakon raya wurin.” To, zan so in fada wa wadannan mutane cewa, idan ka samu damar karanta takardar bayanin da kasar Sin ta fitar a kwanan baya, wadda ta shafi tunanin kasar na raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, tabbas za ka samu wani ra’ayi na daban game da kasar ta Sin.

Sai dai mene ne “al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”? Ma’anar ita ce, wani yanayin da ake ciki na samun hadin gwiwar mabambantan al’ummu da kasashe, inda suke tinkarar kalubaloli tare, da neman samun ci gaba na bai daya. Samun wannan yanayi shi ne babban burin kasar Sin ta fuskar hulda da sauran kasashe. Saboda haka, a lokacin da kasar Sin take ciniki da kasashen Afirka, da zuba jari a kasashen, da gaske ne tana neman samun cin moriya tare da kasashen Afirka, gami da ci gaba na bai daya. Yayin da matakan kwashe albarkatun wasu kasashe, da hana sauran kasashe ci gaba don neman kare matsayin wata kasa, suka saba da tushen tunanin Sinawa a fannin diplomasiyya.

  • Tawagar Masu Aikin Na’urar Binciken Duniyar Wata Mai Suna Chang’e 5 Ta Kasar Sin Ta Samu Babbar Lambar Yabo
  • Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

To, mene ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ba da shawarar raya al’ummar dan Adam mai makomar bai daya? Dalili na farko shi ne, al’adun kasar na darajanta zaman lafiya, da neman samun daidaito tsakanin al’umma. Wannan al’adu ya zo daya da tunanin Ubuntu na Afirka, wanda ya jaddada muhimmancin dogaro da juna da hadin gwiwa a tsakanin mutane.

Sa’an nan wani dalili na daban shi ne yadda kasar Sin ta san ainihin abun da duniyarmu ke bukata, gami da makomarta a nan gaba. Duniyarmu tana fuskantar dimbin matsalolin da suka hada da koma bayan tattalin arziki, da gibin da ake samu a fannin raya kasa, da yake-yake, da lalacewar muhalli, da ta’addanci, da dai sauransu. Duk da haka, wasu kasashen dake yammacin duniya na ci gaba da yunkurin daukar matakan kashin dankali, da kulla kawance don jayayya da wasu, da yin babakere a duniya, wadanda tarihi ya riga ya shaida kuskurensu. To, me ya sa ake son maimaita kuskure? Abun da duniyarmu ke bukata, shi ne a daidaita matsalolin da ake fuskanta daga tushe, maimakon tura su zuwa sauran kasashe. Ganin haka ya sa kasar Sin ta gabatar da ra’ayin raya al’ummar dan Adam mai makomar bai daya, wanda ya daukaka hadin gwiwa, da cin moriya tare, gami da samun ci gaba na bai daya.

Tabbas, idan mun yi ihun cewa “Bari mu yi hadin gwiwa” kawai, maimakon daukar hakikanin mataki, to, ba zai yi amfani ba ko kadan. Amma sabanin haka, tunanin kasar Sin na raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya ya kunshi dimbin dabaru da manufofin da ake kokarin aiwatar da su. Inda dabarun suka hada da tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya, gami da daukaka ra’ayoyi na bude kofa ga ketare, da lura da moriyar kowa, da amfanawa juna, da samun daidaito, da wanzar da zaman lafiya yayin da ake kokarin raya kasa, da raya huldar kasa da kasa bisa daidaito, da adalci, da hadin kai, gami da daukaka ra’ayin samun bangarori masu fada a ji da yawa a duniya, da dai sauransu. Kana manufofin da ake aiwatar da su sun hada da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, da matakan aiwatar da shawarwari na tabbatar da ci gaba, da tsaro, da raya wayewar kai a duniya, da dai makamantansu.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

A karshe, ina so in ce, tunanin Sin na raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya yana da ma’anar musamman ga huldar dake tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin. Saboda al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ta Sin da Afirka irinta ce ta farko da aka gabatar a duniya. Kana halayen huldar dake tsakanin Sin da Afirka na nuna sahihanci, da zumunta, da zaman daidaiwa daida, da mai da adalci a gaban moriya, da kokarin biyan bukatun jama’a, da daukar hakikanan matakai masu amfani ba tare da bata lokaci ba, su ma sun tabbatar da matsayin hadin gwiwar Sin da Afirka na abin koyi a fannin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya a duniya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Li QiangPeng LiyuanXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

ISWAP Ta Hallaka Kwamandan Boko Haram A Sambisa

Next Post

Farfesan Farfesoshi, Tsohon Mataimakin Shugaban Jami’ar Nsukka, Emeritus Umaru Shehu, Ya Rasu

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

19 minutes ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

2 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

2 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

6 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

8 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

8 hours ago
Next Post
Emeritus Umaru Shehu

Farfesan Farfesoshi, Tsohon Mataimakin Shugaban Jami'ar Nsukka, Emeritus Umaru Shehu, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.