ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Takarda Ta Nuna Burin Kasar Sin A Fannin Hulda Da Sauran Kasashe

by CGTN Hausa
3 years ago
Kasar sin

Da nake karanta bayanan da aka rubuta a Facebook, na ga yawancin bayanai masu alaka da huldar dake tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin sun nuna wani yanayi mai yakini da yabo. Sai dai ra’ayi riga, ba za a rasa wani mutum mai dauke da wani ra’ayi na daban ba. Misali, a ganin wasu mutane, wai “Sinawa sun yi kama da Turawa, sun je nahiyar Afirka don kwashe albarkatu maimakon raya wurin.” To, zan so in fada wa wadannan mutane cewa, idan ka samu damar karanta takardar bayanin da kasar Sin ta fitar a kwanan baya, wadda ta shafi tunanin kasar na raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, tabbas za ka samu wani ra’ayi na daban game da kasar ta Sin.

Sai dai mene ne “al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”? Ma’anar ita ce, wani yanayin da ake ciki na samun hadin gwiwar mabambantan al’ummu da kasashe, inda suke tinkarar kalubaloli tare, da neman samun ci gaba na bai daya. Samun wannan yanayi shi ne babban burin kasar Sin ta fuskar hulda da sauran kasashe. Saboda haka, a lokacin da kasar Sin take ciniki da kasashen Afirka, da zuba jari a kasashen, da gaske ne tana neman samun cin moriya tare da kasashen Afirka, gami da ci gaba na bai daya. Yayin da matakan kwashe albarkatun wasu kasashe, da hana sauran kasashe ci gaba don neman kare matsayin wata kasa, suka saba da tushen tunanin Sinawa a fannin diplomasiyya.

  • Tawagar Masu Aikin Na’urar Binciken Duniyar Wata Mai Suna Chang’e 5 Ta Kasar Sin Ta Samu Babbar Lambar Yabo
  • Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

To, mene ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ba da shawarar raya al’ummar dan Adam mai makomar bai daya? Dalili na farko shi ne, al’adun kasar na darajanta zaman lafiya, da neman samun daidaito tsakanin al’umma. Wannan al’adu ya zo daya da tunanin Ubuntu na Afirka, wanda ya jaddada muhimmancin dogaro da juna da hadin gwiwa a tsakanin mutane.

ADVERTISEMENT

Sa’an nan wani dalili na daban shi ne yadda kasar Sin ta san ainihin abun da duniyarmu ke bukata, gami da makomarta a nan gaba. Duniyarmu tana fuskantar dimbin matsalolin da suka hada da koma bayan tattalin arziki, da gibin da ake samu a fannin raya kasa, da yake-yake, da lalacewar muhalli, da ta’addanci, da dai sauransu. Duk da haka, wasu kasashen dake yammacin duniya na ci gaba da yunkurin daukar matakan kashin dankali, da kulla kawance don jayayya da wasu, da yin babakere a duniya, wadanda tarihi ya riga ya shaida kuskurensu. To, me ya sa ake son maimaita kuskure? Abun da duniyarmu ke bukata, shi ne a daidaita matsalolin da ake fuskanta daga tushe, maimakon tura su zuwa sauran kasashe. Ganin haka ya sa kasar Sin ta gabatar da ra’ayin raya al’ummar dan Adam mai makomar bai daya, wanda ya daukaka hadin gwiwa, da cin moriya tare, gami da samun ci gaba na bai daya.

Tabbas, idan mun yi ihun cewa “Bari mu yi hadin gwiwa” kawai, maimakon daukar hakikanin mataki, to, ba zai yi amfani ba ko kadan. Amma sabanin haka, tunanin kasar Sin na raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya ya kunshi dimbin dabaru da manufofin da ake kokarin aiwatar da su. Inda dabarun suka hada da tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya, gami da daukaka ra’ayoyi na bude kofa ga ketare, da lura da moriyar kowa, da amfanawa juna, da samun daidaito, da wanzar da zaman lafiya yayin da ake kokarin raya kasa, da raya huldar kasa da kasa bisa daidaito, da adalci, da hadin kai, gami da daukaka ra’ayin samun bangarori masu fada a ji da yawa a duniya, da dai sauransu. Kana manufofin da ake aiwatar da su sun hada da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, da matakan aiwatar da shawarwari na tabbatar da ci gaba, da tsaro, da raya wayewar kai a duniya, da dai makamantansu.

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

A karshe, ina so in ce, tunanin Sin na raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya yana da ma’anar musamman ga huldar dake tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin. Saboda al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ta Sin da Afirka irinta ce ta farko da aka gabatar a duniya. Kana halayen huldar dake tsakanin Sin da Afirka na nuna sahihanci, da zumunta, da zaman daidaiwa daida, da mai da adalci a gaban moriya, da kokarin biyan bukatun jama’a, da daukar hakikanan matakai masu amfani ba tare da bata lokaci ba, su ma sun tabbatar da matsayin hadin gwiwar Sin da Afirka na abin koyi a fannin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya a duniya. (Bello Wang)

Kasar sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
Daga Birnin Sin

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
Daga Birnin Sin

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
Next Post
Emeritus Umaru Shehu

Farfesan Farfesoshi, Tsohon Mataimakin Shugaban Jami'ar Nsukka, Emeritus Umaru Shehu, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.