• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya sanya hannu a hukumance kan kudurin da zai sa kaimi ga samar da shawarwari kan batun Xizang (wato Tibet) da Sin, a ranar 12 ga watan Yuli, wanda ya nuna cewa, gwamnatin Amurka ba ta taba daukar matsayin cewa Xizang yanki ne na kasar Sin ba tun a zamanin da, da cewa dole ne a warware sabani tsakanin Xizang da kasar Sin ta hanyar lumana bisa dokokin kasa da kasa ta hanyar tattaunawa ba tare da wani sharadi ba. 

Wannan wasan karta fakewa ne da guzuma don a harbi karsana, da kuma tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Yankin Xizang mai cin gashin kansa wani bangare ne na kasar Sin tun fil azal, kuma harkokin Xizang lamari ne na cikin gida na kasar Sin, wanda ba ya bukatar tsangwama daga wani bangare daga waje. Binciken kayan tarihi da aka yi a wannan yanki na kudu maso yammacin kasar Sin ya nuna dadadden alaka mai karfi da kusanci tsakaninsa da sauran yankunan kasar Sin, wanda ya tabbatar da hadin kan al’ummar kasar Sin mai mabambantan al’adu.

  • Masana Sun Yi Kira Da A Fadada Musayar Al’adu Da Yawon Shakatawa Tsakanin Sin Da Najeriya
  • Shugaban Kasar Sin Ya Jajantawa Donald Trump

Misali, daga cikin kayayyakin tarihi da aka gano a kabarin Guru Jiamu da ke Ali, a wannan yanki, wanda ya samo asali ne daga daular Han ta Gabas kimanin shekaru 2,000 da suka gabata, akwai wani kayan surfani da ya kwashe sama da shekaru 1,800 da suka gabata wanda aka tsara da zanen tsuntsaye da namomin jeji, yana dauke da harafin Sinanci “wanghou,” ma’ana girma, kuma shi ne kayan tarihi na siliki na farko da aka samu a kan tudun Qinghai-Xizang, wanda ya tabbatar da dogon tarihin mu’amalar kud-da-kud tsakanin yankin da sauran sassa da kabilun kasar.

Kokarin gurbata gaskiya ta hanyar kafa dokokin cikin gida kuma bisa radin kai da kuma musanta tarihin cewa Xizang wani bangare ne na kasar Sin tun a zamanin da, wata dabara ce mai cike da rudani don bata wa kasar Sin mutuncinta. Dole ne Amurka ta mutunta ka’idar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”, ta kuma daina goyon bayan duk wani nau’i na neman “yancin kai na Xizang”, da kuma janye sabuwar dokarta ta tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Tabbas wannan yunkurin karkata gaskiya zai gaza, kuma zai fuskanci adawa ba da kasar Sin kawai ba, har ma da daga sauran kasashen duniya. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ministan Yaɗa Labarai Ya Karɓi Baƙuncin ‘Yan Jaridar Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Next Post

Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

Related

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

15 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

16 hours ago
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

17 hours ago
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

2 days ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 days ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

2 days ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

LABARAI MASU NASABA

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

August 11, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

August 11, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.