• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya sanya hannu a hukumance kan kudurin da zai sa kaimi ga samar da shawarwari kan batun Xizang (wato Tibet) da Sin, a ranar 12 ga watan Yuli, wanda ya nuna cewa, gwamnatin Amurka ba ta taba daukar matsayin cewa Xizang yanki ne na kasar Sin ba tun a zamanin da, da cewa dole ne a warware sabani tsakanin Xizang da kasar Sin ta hanyar lumana bisa dokokin kasa da kasa ta hanyar tattaunawa ba tare da wani sharadi ba. 

Wannan wasan karta fakewa ne da guzuma don a harbi karsana, da kuma tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Yankin Xizang mai cin gashin kansa wani bangare ne na kasar Sin tun fil azal, kuma harkokin Xizang lamari ne na cikin gida na kasar Sin, wanda ba ya bukatar tsangwama daga wani bangare daga waje. Binciken kayan tarihi da aka yi a wannan yanki na kudu maso yammacin kasar Sin ya nuna dadadden alaka mai karfi da kusanci tsakaninsa da sauran yankunan kasar Sin, wanda ya tabbatar da hadin kan al’ummar kasar Sin mai mabambantan al’adu.

  • Masana Sun Yi Kira Da A Fadada Musayar Al’adu Da Yawon Shakatawa Tsakanin Sin Da Najeriya
  • Shugaban Kasar Sin Ya Jajantawa Donald Trump

Misali, daga cikin kayayyakin tarihi da aka gano a kabarin Guru Jiamu da ke Ali, a wannan yanki, wanda ya samo asali ne daga daular Han ta Gabas kimanin shekaru 2,000 da suka gabata, akwai wani kayan surfani da ya kwashe sama da shekaru 1,800 da suka gabata wanda aka tsara da zanen tsuntsaye da namomin jeji, yana dauke da harafin Sinanci “wanghou,” ma’ana girma, kuma shi ne kayan tarihi na siliki na farko da aka samu a kan tudun Qinghai-Xizang, wanda ya tabbatar da dogon tarihin mu’amalar kud-da-kud tsakanin yankin da sauran sassa da kabilun kasar.

Kokarin gurbata gaskiya ta hanyar kafa dokokin cikin gida kuma bisa radin kai da kuma musanta tarihin cewa Xizang wani bangare ne na kasar Sin tun a zamanin da, wata dabara ce mai cike da rudani don bata wa kasar Sin mutuncinta. Dole ne Amurka ta mutunta ka’idar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”, ta kuma daina goyon bayan duk wani nau’i na neman “yancin kai na Xizang”, da kuma janye sabuwar dokarta ta tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Tabbas wannan yunkurin karkata gaskiya zai gaza, kuma zai fuskanci adawa ba da kasar Sin kawai ba, har ma da daga sauran kasashen duniya. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ministan Yaɗa Labarai Ya Karɓi Baƙuncin ‘Yan Jaridar Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Next Post

Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

Related

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

1 hour ago
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

3 hours ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

3 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

5 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

5 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

7 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.