• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasikun Xi Jinping Ga Matasa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wasikun Xi Jinping Ga Matasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matasa su ne makomar kasa. Tun da dadewa, shugaban kasar Sin Xi Jinping yake nuna kulawar musamman game da ci gaban matasa, kuma sau da yawa yana tattaunawa da matasa ta hanyar wasiku.

A watan Yuni na shekarar 2003, Lin Dongmei, wata yarinya daga lardin Fujian dake kudu maso gabashin kasar Sin, ta samu wasika daga Xi Jinping, wanda shi ne daraktan kwamitin jam’iyyar JKS reshen lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin, a lokacin.

  • Sin: Duk Mai Kokarin Hana Ci Gaban Tarihi Ba Zai Yi Nasara Ba

A shekara ta 1994, ta hanyar aikin jin kai na “Project Hope”, Xi Jinping ya hadu da Lin Dongmei, yariniyar dake fama da talauci.

A cikin shekaru 12 da suka biyo baya, Xi Jinping ya yi amfani da wani bangare na albashinsa wajen tallafa mata a kowace shekara, tun tana aji hudu a makarantar firamare har ta kammala karatu a jami’a.

A cikin shekaru fiye da goma da suka gabata, daga karatu zuwa aiki, daga karamar yarinya zuwa matashiya, Lin Dongmei ta samu jimillar wasiku biyar daga Xi Jinping.

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Kalmomi gajeru ne amma suna da ma’ana, kuma sun jagoranci hanyar ci gaban Lin Dongmei. Yanzu, bayan da ta yi aiki na fiye da shekaru 10, Lin Dongmei tana kashe akalla albashin wata guda a kowace shekara wajen taimaka wa talakawa don samar musu da makoma mai haske.

Daga cikin abokan sa da su kan rubuta wasiku ga juna da Xi Jinping, akwai kuma matasan kasashen waje da dama.

A ranar 17 ga watan Mayu na shekarar 2020, Xi Jinping ya rubuta wasika ga dukkan daliban Pakistan dake karatu a jami’ar kimiyya da fasaha ta Beijing, inda ya yi maraba ga fitattun matasa daga kasashe daban daban don su yi karatu a kasar Sin.

Ya kara karfafa musu gwiwa da su kara yin mu’amala da matasan kasar Sin, da yin kokari tare da matasa daga ko’ina cikin duniya don ba da gudummawarsu wajen inganta cudanya tsakanin jama’a da gina al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga daukacin bil-Adam.

Akwai wasiku da yawa da Xi Jinping ya rubuta ga matasa, wanda hakan ya zaburar da su, su yi aiki tukuru. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Sanya Lokacin Da Za A Yi Kidayar 2023

Next Post

‘Yan IPOB 9 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Kashe ‘Yansanda A Imo

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

4 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

5 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

6 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

7 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

8 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

9 hours ago
Next Post
Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti

'Yan IPOB 9 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Kashe 'Yansanda A Imo

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.