• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Matan

Dakta Hadiza Balarabe

Matan

Hadiza Sabuwa Balarabe, ‘yar siyasa ce kuma likita wadda ta kafa tarihi a shekarar 2019, inda ta zama Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna. Har ila yau, ita ce mace ta farko da ta fara zama Maitaimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, sannan inda ta ci gaba da yin wannan aiki bisa sadaukarwarta.

Har wa yau, a matsayinta na kwararriyar likitar; kuma mai ba da shawara sakamakon kwarewar da take da ita a fannin sama da shekaru ashirin, Dakta Hadiza Balarabe; ta bayar da gudummawa sosai wajen inganta harkokin kiwon lafiya a Nijeriya.

Ta fara aiki a shekarar 1990, a babban asibitin Wuse da ke Abuja, inda ta yi aiki a matsayin babbar jami’ar lafiya, daga nan kuma ta yi ayyuka daban-daban a asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, kafin ta ki ga samun mukamin shugabanci a fannin kiwon lafiya na jama’a, ciki har da daraktar kula da lafiyar jama’a a Babban Birnin Tarayya Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

A shekarar 2019, ta gabatar wa Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, sabon kasafin kudin shekarar 2020 a madadin gwamnan, inda ta zama mace ta farko da ta yi hakan a Arewacin Nijeriya.

Bugu da kari, Dakta Balarabe ta ci gaba da kasancewa mai mutukar himma a cikin shirye-shiryen karfafa al’umma da shawarwari. Sannan, ta kasance mai daidaita al’umma tare da karfafa matasa, domin ci gabansu mai dorewa.

Hajara Adeola

Matan

Hajara Adeola kuma, ita ce Shugabar Bankin LOTUS (LOTUS Bank Limited), ta kuma rike matsayin shugaba kuma Darakta a Kamfanin Lotus Capital (Lotus Capital Limited), wani kamfani na Nijeriya; wanda ya shahara da aikinsa na farko a harkar sarrafa kadarorin Shari’a, ayyukan ba da shawarwari na sarrafa dukiya da harkokin kudi.

 Kafin Bankin LOTUS da kuma Kamfanin na Lotus Capital, Adeola ta rike manyan mukamai a manyan cibiyoyin hada-hadar kudi, musamman, inda ta yi aiki a matsayin Daraktar ‘CCT Islamic Finance a UBS Warburg’, inda take kula da asusun kudin Musulunci na Landan. Sannan kuma, ta yi fice a matsayin Manazarciyar Binciken Hadin Kan Muhimmai a BNP Paribas da London.

Adeola ta zama shugaba ta farko, a kungiyar ma’ajiyoyin Nijeriya. Dangane da matsayin da take rike da shi a halin yanzu, Adeola ta shugabanci kwamitin tsare-tsaren babbar kasuwar hannun jari da babu ruwa a cikinsa tsawon shekara 10, kazalika mace ce mai son ci gaba; wajen habaka harkokin kasuwanci.

Bugu da kari, Adeola Darakta ce a Gidauniyar Aliko Dangote, inda ta dukufa sosai ga ayyukan jin kai tare da ci gaban al’umma baki-daya.

Ambasada Fatima Kyari Mohammed

Matan

 Ambasada Fatima Kyari Mohammed, Babbar Jami’ar Tarayyar Afirka Mai Sa Ido a Majalisar Dinkin Duniya. Kafin a ba ta wannan mukami, ta kasance babbar mai ba da shawara ta musamman ga Kungiyar Bunkasa Tattalin Arziki ta Yammacin Afirka (ECOWAS), tare da wanzar da zaman lafiya da tsaro a yankin da kuma ci gaban kungiyoyi.

 Ta kuma yi aiki a matsayin Babbar Daraktar Tuntuba kan Tsaro da Sulhu a Afirka ta Yamma ‘Conflict and Security Consulting’. Sannan ta yi aiki a matsayin Manajar Shirye-shirye a Tawagar Tarayyar Turai a Nijeriya da ECOWAS, sannan kuma ta rike mukamin Manajar Ayyuka ta Yanki da Tsaro a Afirka.

 Ambasada Fatima Kyari, ita ce wacce ta kafa wata kungiya mai zaman kanta (LikeMinds), haka zalika; ta sadaukar da kanta wajen taimaka wa al’umma daban-daban musamman masu rauni a Nijeriya. Wannan kungiya da ta kafa, tana karfafa wa mata da matasa guiwa tare da bayar da tallafi ga marayu da yara masu rauni.

 Har ila yau, Ambasada Fatima; ta ba da gudunmawa matuka wajen samar da zaman lafiya. Sannan, an amince da ita a matsayin daya daga cikin mata 100 mafi tasiri cikin matan Afirka ta hanyar yin amfani da kafafen yada labarai (Abance Media) a shekarar 2021 da 2022. Haka zalika, kungiyar ‘NCWG International’ ta zabe ta, ta kuma karrama ta a matsayin macen da take son kawo zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Halima Ibrahim Abba

Matan

Halima Ibrahim Abba, kwararriya ce a fannin harkokin kudi; wacce ta shafe sama da shekaru 13 a ciki, sannan kuma shugabar Gidauniyar ‘Skills Outside School Foundation’, wacce ta yi fice a Afirka, kana kuma tana matukar yin kokari wajen samar da aikin yi da kasuwanci, tana kuma bayar da shawarwarin bayanai da na dabaru tare da abokan tarayya da jajircewa a duk fadin Nijeriya da sauran makamantansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Next Post
Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.