• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakta Hadiza Balarabe

Matan

Hadiza Sabuwa Balarabe, ‘yar siyasa ce kuma likita wadda ta kafa tarihi a shekarar 2019, inda ta zama Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna. Har ila yau, ita ce mace ta farko da ta fara zama Maitaimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, sannan inda ta ci gaba da yin wannan aiki bisa sadaukarwarta.

Har wa yau, a matsayinta na kwararriyar likitar; kuma mai ba da shawara sakamakon kwarewar da take da ita a fannin sama da shekaru ashirin, Dakta Hadiza Balarabe; ta bayar da gudummawa sosai wajen inganta harkokin kiwon lafiya a Nijeriya.

Ta fara aiki a shekarar 1990, a babban asibitin Wuse da ke Abuja, inda ta yi aiki a matsayin babbar jami’ar lafiya, daga nan kuma ta yi ayyuka daban-daban a asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, kafin ta ki ga samun mukamin shugabanci a fannin kiwon lafiya na jama’a, ciki har da daraktar kula da lafiyar jama’a a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

A shekarar 2019, ta gabatar wa Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, sabon kasafin kudin shekarar 2020 a madadin gwamnan, inda ta zama mace ta farko da ta yi hakan a Arewacin Nijeriya.

Bugu da kari, Dakta Balarabe ta ci gaba da kasancewa mai mutukar himma a cikin shirye-shiryen karfafa al’umma da shawarwari. Sannan, ta kasance mai daidaita al’umma tare da karfafa matasa, domin ci gabansu mai dorewa.

Hajara Adeola

Matan

Hajara Adeola kuma, ita ce Shugabar Bankin LOTUS (LOTUS Bank Limited), ta kuma rike matsayin shugaba kuma Darakta a Kamfanin Lotus Capital (Lotus Capital Limited), wani kamfani na Nijeriya; wanda ya shahara da aikinsa na farko a harkar sarrafa kadarorin Shari’a, ayyukan ba da shawarwari na sarrafa dukiya da harkokin kudi.

 Kafin Bankin LOTUS da kuma Kamfanin na Lotus Capital, Adeola ta rike manyan mukamai a manyan cibiyoyin hada-hadar kudi, musamman, inda ta yi aiki a matsayin Daraktar ‘CCT Islamic Finance a UBS Warburg’, inda take kula da asusun kudin Musulunci na Landan. Sannan kuma, ta yi fice a matsayin Manazarciyar Binciken Hadin Kan Muhimmai a BNP Paribas da London.

Adeola ta zama shugaba ta farko, a kungiyar ma’ajiyoyin Nijeriya. Dangane da matsayin da take rike da shi a halin yanzu, Adeola ta shugabanci kwamitin tsare-tsaren babbar kasuwar hannun jari da babu ruwa a cikinsa tsawon shekara 10, kazalika mace ce mai son ci gaba; wajen habaka harkokin kasuwanci.

Bugu da kari, Adeola Darakta ce a Gidauniyar Aliko Dangote, inda ta dukufa sosai ga ayyukan jin kai tare da ci gaban al’umma baki-daya.

Ambasada Fatima Kyari Mohammed

Matan

 Ambasada Fatima Kyari Mohammed, Babbar Jami’ar Tarayyar Afirka Mai Sa Ido a Majalisar Dinkin Duniya. Kafin a ba ta wannan mukami, ta kasance babbar mai ba da shawara ta musamman ga Kungiyar Bunkasa Tattalin Arziki ta Yammacin Afirka (ECOWAS), tare da wanzar da zaman lafiya da tsaro a yankin da kuma ci gaban kungiyoyi.

 Ta kuma yi aiki a matsayin Babbar Daraktar Tuntuba kan Tsaro da Sulhu a Afirka ta Yamma ‘Conflict and Security Consulting’. Sannan ta yi aiki a matsayin Manajar Shirye-shirye a Tawagar Tarayyar Turai a Nijeriya da ECOWAS, sannan kuma ta rike mukamin Manajar Ayyuka ta Yanki da Tsaro a Afirka.

 Ambasada Fatima Kyari, ita ce wacce ta kafa wata kungiya mai zaman kanta (LikeMinds), haka zalika; ta sadaukar da kanta wajen taimaka wa al’umma daban-daban musamman masu rauni a Nijeriya. Wannan kungiya da ta kafa, tana karfafa wa mata da matasa guiwa tare da bayar da tallafi ga marayu da yara masu rauni.

 Har ila yau, Ambasada Fatima; ta ba da gudunmawa matuka wajen samar da zaman lafiya. Sannan, an amince da ita a matsayin daya daga cikin mata 100 mafi tasiri cikin matan Afirka ta hanyar yin amfani da kafafen yada labarai (Abance Media) a shekarar 2021 da 2022. Haka zalika, kungiyar ‘NCWG International’ ta zabe ta, ta kuma karrama ta a matsayin macen da take son kawo zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Halima Ibrahim Abba

Matan

Halima Ibrahim Abba, kwararriya ce a fannin harkokin kudi; wacce ta shafe sama da shekaru 13 a ciki, sannan kuma shugabar Gidauniyar ‘Skills Outside School Foundation’, wacce ta yi fice a Afirka, kana kuma tana matukar yin kokari wajen samar da aikin yi da kasuwanci, tana kuma bayar da shawarwarin bayanai da na dabaru tare da abokan tarayya da jajircewa a duk fadin Nijeriya da sauran makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Ta Bankado Sunaye 15 Da Ake Zargi Da Hannu A Tallafa Wa Ta’addanci

Next Post

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

1 month ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

2 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

5 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

5 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

7 months ago
Next Post
Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.