ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Matan

Dakta Hadiza Balarabe

Matan

Hadiza Sabuwa Balarabe, ‘yar siyasa ce kuma likita wadda ta kafa tarihi a shekarar 2019, inda ta zama Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna. Har ila yau, ita ce mace ta farko da ta fara zama Maitaimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, sannan inda ta ci gaba da yin wannan aiki bisa sadaukarwarta.

ADVERTISEMENT

Har wa yau, a matsayinta na kwararriyar likitar; kuma mai ba da shawara sakamakon kwarewar da take da ita a fannin sama da shekaru ashirin, Dakta Hadiza Balarabe; ta bayar da gudummawa sosai wajen inganta harkokin kiwon lafiya a Nijeriya.

Ta fara aiki a shekarar 1990, a babban asibitin Wuse da ke Abuja, inda ta yi aiki a matsayin babbar jami’ar lafiya, daga nan kuma ta yi ayyuka daban-daban a asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, kafin ta ki ga samun mukamin shugabanci a fannin kiwon lafiya na jama’a, ciki har da daraktar kula da lafiyar jama’a a Babban Birnin Tarayya Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

A shekarar 2019, ta gabatar wa Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, sabon kasafin kudin shekarar 2020 a madadin gwamnan, inda ta zama mace ta farko da ta yi hakan a Arewacin Nijeriya.

Bugu da kari, Dakta Balarabe ta ci gaba da kasancewa mai mutukar himma a cikin shirye-shiryen karfafa al’umma da shawarwari. Sannan, ta kasance mai daidaita al’umma tare da karfafa matasa, domin ci gabansu mai dorewa.

Hajara Adeola

Matan

Hajara Adeola kuma, ita ce Shugabar Bankin LOTUS (LOTUS Bank Limited), ta kuma rike matsayin shugaba kuma Darakta a Kamfanin Lotus Capital (Lotus Capital Limited), wani kamfani na Nijeriya; wanda ya shahara da aikinsa na farko a harkar sarrafa kadarorin Shari’a, ayyukan ba da shawarwari na sarrafa dukiya da harkokin kudi.

 Kafin Bankin LOTUS da kuma Kamfanin na Lotus Capital, Adeola ta rike manyan mukamai a manyan cibiyoyin hada-hadar kudi, musamman, inda ta yi aiki a matsayin Daraktar ‘CCT Islamic Finance a UBS Warburg’, inda take kula da asusun kudin Musulunci na Landan. Sannan kuma, ta yi fice a matsayin Manazarciyar Binciken Hadin Kan Muhimmai a BNP Paribas da London.

Adeola ta zama shugaba ta farko, a kungiyar ma’ajiyoyin Nijeriya. Dangane da matsayin da take rike da shi a halin yanzu, Adeola ta shugabanci kwamitin tsare-tsaren babbar kasuwar hannun jari da babu ruwa a cikinsa tsawon shekara 10, kazalika mace ce mai son ci gaba; wajen habaka harkokin kasuwanci.

Bugu da kari, Adeola Darakta ce a Gidauniyar Aliko Dangote, inda ta dukufa sosai ga ayyukan jin kai tare da ci gaban al’umma baki-daya.

Ambasada Fatima Kyari Mohammed

Matan

 Ambasada Fatima Kyari Mohammed, Babbar Jami’ar Tarayyar Afirka Mai Sa Ido a Majalisar Dinkin Duniya. Kafin a ba ta wannan mukami, ta kasance babbar mai ba da shawara ta musamman ga Kungiyar Bunkasa Tattalin Arziki ta Yammacin Afirka (ECOWAS), tare da wanzar da zaman lafiya da tsaro a yankin da kuma ci gaban kungiyoyi.

 Ta kuma yi aiki a matsayin Babbar Daraktar Tuntuba kan Tsaro da Sulhu a Afirka ta Yamma ‘Conflict and Security Consulting’. Sannan ta yi aiki a matsayin Manajar Shirye-shirye a Tawagar Tarayyar Turai a Nijeriya da ECOWAS, sannan kuma ta rike mukamin Manajar Ayyuka ta Yanki da Tsaro a Afirka.

 Ambasada Fatima Kyari, ita ce wacce ta kafa wata kungiya mai zaman kanta (LikeMinds), haka zalika; ta sadaukar da kanta wajen taimaka wa al’umma daban-daban musamman masu rauni a Nijeriya. Wannan kungiya da ta kafa, tana karfafa wa mata da matasa guiwa tare da bayar da tallafi ga marayu da yara masu rauni.

 Har ila yau, Ambasada Fatima; ta ba da gudunmawa matuka wajen samar da zaman lafiya. Sannan, an amince da ita a matsayin daya daga cikin mata 100 mafi tasiri cikin matan Afirka ta hanyar yin amfani da kafafen yada labarai (Abance Media) a shekarar 2021 da 2022. Haka zalika, kungiyar ‘NCWG International’ ta zabe ta, ta kuma karrama ta a matsayin macen da take son kawo zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Halima Ibrahim Abba

Matan

Halima Ibrahim Abba, kwararriya ce a fannin harkokin kudi; wacce ta shafe sama da shekaru 13 a ciki, sannan kuma shugabar Gidauniyar ‘Skills Outside School Foundation’, wacce ta yi fice a Afirka, kana kuma tana matukar yin kokari wajen samar da aikin yi da kasuwanci, tana kuma bayar da shawarwarin bayanai da na dabaru tare da abokan tarayya da jajircewa a duk fadin Nijeriya da sauran makamantansu.

Matan
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.