ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

by Ibrahim Bala
2 years ago
Rayuwa

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Muna rokon Allah ya ba mu alhairan da ke cikin wannan wata mai girma na Ramadana.

Jan hankalin da zan yi tare da tunatarwa a yau, a kan iyaye maza da mata da kuma su kansu ‘ya’ya ne, sannan da kuma yayye wadanda ke kasancewa a matsayin magadan uba, da kuma wadanda ke da kanne mata.

ADVERTISEMENT

Hakika mun shiga wani irin yanayi na kuncin rayuwa, wanda iyaye ba lallai ba ne su iya yi wa ‘ya’yansu abubuwan da suke bukata ba, musamman a bangaren da ya shafi dinkunan sallah da sauran makamantansu.

Don haka, yana da matukar muhimmanci iyaye su sa ido a kan ‘ya’yansu, su kuma kula sosai wajen ganin da me da me yarinya ta shigo gida da me kuma ta fita? Ka da ‘yarka ko ‘yarki ko kanwarka ta rika shigowa gida da kayayyakin dinki da sunan saurayi ne ya ba ta ta kuma karba, ba tare da kun yi bincike ba, har sai wani abu ya je ya zo; sannan a fara neman mafitar da za ta yi wuyar samu.

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Ba don komai na ce haka ba, sai don sanin yadda dabi’un wasu mazan take a halin yanzu, wasu ba su da kirki ko kadan; domin kuwa za su iya amfani da halin da ake ciki na kuncin rayuwa a kan atamfa kadai ko shadda ko takalmi ko wani abu da yarinya za ta saka da sallah, su lalata mata rayuwa.

Don haka, dole ne a mayar da hankali kwarai da gaske a kansu, sannan duk abin da ta kawo; ya kamata a san wanda ya bayar a kuma ji dalilin bayarwar. Kazalika, idan abin aka ga ya yi yawa ma sai a bincika a dalili, tunda ita ba ‘yar sarki ba ce; iyakar abin da Allah ya hore iyaye a yi hakuri da shi, sannan kuma ku ja wa ‘ya’yanku kunne, saboda yanzu ‘yan mata suna da irin wannan hangen, yarinya za ta ga waya a hannun wata; sai ta saka abin a ranta cewa; ya kamata ita ma ta rike irin ta da sallah, ko da kuwa ta halin kaka ne.

Haka nan, idan ta ga kaya ko jallabiya ko riga ko wani abu dai makamancin irin wannan a hannun kawayenta, ita ma sai ta ce lallai sai ta samu, kar ka yarda a matsayinka na uba ko a matsayinki na uwa, idan an kawo irin wannan ki yi shuru, ya kamata ki binciki asalin abin da yake faruwa.

Kazalika, kai ma da kake a matsayin babban wa na dawo gare ka, lallai ne ka sa ido a kan kannanka sosai, ba zai yiwu don lokacin azumi ne saurayi ya zo ya kai karfe daya ko karfe sha biyu yana tare da kanwarka ba, haka nan yau wannan ya zo, gobe wannan ya zo.

Sannan, yau wannan ya kawo takalmi; gobe wancan ya kawo shadda, jibi kuma wancan ya kawo doguwar riga, dole ne ku sa ido a mayar da hankali ka da a ga cewa ai ana cikin halin ha’ula’i, ko ana cikin wani irin yanayi da iyaye ba za su iya yi wa ‘ya’ya dinkunan da suke so ba, duk abin da Allah ya yassare sai a yi hakuri a karba, ya kamata kuma a lura da cewa; duk abin da ka same shi ta wata hanya ta daban, idan da ka yi hakuri ta hanyar halak ma zai zo ya same ka har inda kake.

Don haka, yanzu lokaci ne na addu’a da ya kamata su kansu samari da ‘yan matan su yi amfani da shi a roki Allah subhanahu wata’ala ya kawo mana sauki da sassauci, idan budurwa ce ki roki Allah ya kawo miki miji nagari, haka nan saurayi shi ma ya roki Allah ya kawo masa mata ta gari.

A takaice, wannan shi ne jan hankalina da fatan Allah ya sa za mu sa ido yadda ya kamata, Allah ya sa mu dace, amin.

Rayuwa
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (4)

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (4)

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.