ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

by Ibrahim Bala
2 years ago
Rayuwa

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Muna rokon Allah ya ba mu alhairan da ke cikin wannan wata mai girma na Ramadana.

Jan hankalin da zan yi tare da tunatarwa a yau, a kan iyaye maza da mata da kuma su kansu ‘ya’ya ne, sannan da kuma yayye wadanda ke kasancewa a matsayin magadan uba, da kuma wadanda ke da kanne mata.

ADVERTISEMENT

Hakika mun shiga wani irin yanayi na kuncin rayuwa, wanda iyaye ba lallai ba ne su iya yi wa ‘ya’yansu abubuwan da suke bukata ba, musamman a bangaren da ya shafi dinkunan sallah da sauran makamantansu.

Don haka, yana da matukar muhimmanci iyaye su sa ido a kan ‘ya’yansu, su kuma kula sosai wajen ganin da me da me yarinya ta shigo gida da me kuma ta fita? Ka da ‘yarka ko ‘yarki ko kanwarka ta rika shigowa gida da kayayyakin dinki da sunan saurayi ne ya ba ta ta kuma karba, ba tare da kun yi bincike ba, har sai wani abu ya je ya zo; sannan a fara neman mafitar da za ta yi wuyar samu.

LABARAI MASU NASABA

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

Ba don komai na ce haka ba, sai don sanin yadda dabi’un wasu mazan take a halin yanzu, wasu ba su da kirki ko kadan; domin kuwa za su iya amfani da halin da ake ciki na kuncin rayuwa a kan atamfa kadai ko shadda ko takalmi ko wani abu da yarinya za ta saka da sallah, su lalata mata rayuwa.

Don haka, dole ne a mayar da hankali kwarai da gaske a kansu, sannan duk abin da ta kawo; ya kamata a san wanda ya bayar a kuma ji dalilin bayarwar. Kazalika, idan abin aka ga ya yi yawa ma sai a bincika a dalili, tunda ita ba ‘yar sarki ba ce; iyakar abin da Allah ya hore iyaye a yi hakuri da shi, sannan kuma ku ja wa ‘ya’yanku kunne, saboda yanzu ‘yan mata suna da irin wannan hangen, yarinya za ta ga waya a hannun wata; sai ta saka abin a ranta cewa; ya kamata ita ma ta rike irin ta da sallah, ko da kuwa ta halin kaka ne.

Haka nan, idan ta ga kaya ko jallabiya ko riga ko wani abu dai makamancin irin wannan a hannun kawayenta, ita ma sai ta ce lallai sai ta samu, kar ka yarda a matsayinka na uba ko a matsayinki na uwa, idan an kawo irin wannan ki yi shuru, ya kamata ki binciki asalin abin da yake faruwa.

Kazalika, kai ma da kake a matsayin babban wa na dawo gare ka, lallai ne ka sa ido a kan kannanka sosai, ba zai yiwu don lokacin azumi ne saurayi ya zo ya kai karfe daya ko karfe sha biyu yana tare da kanwarka ba, haka nan yau wannan ya zo, gobe wannan ya zo.

Sannan, yau wannan ya kawo takalmi; gobe wancan ya kawo shadda, jibi kuma wancan ya kawo doguwar riga, dole ne ku sa ido a mayar da hankali ka da a ga cewa ai ana cikin halin ha’ula’i, ko ana cikin wani irin yanayi da iyaye ba za su iya yi wa ‘ya’ya dinkunan da suke so ba, duk abin da Allah ya yassare sai a yi hakuri a karba, ya kamata kuma a lura da cewa; duk abin da ka same shi ta wata hanya ta daban, idan da ka yi hakuri ta hanyar halak ma zai zo ya same ka har inda kake.

Don haka, yanzu lokaci ne na addu’a da ya kamata su kansu samari da ‘yan matan su yi amfani da shi a roki Allah subhanahu wata’ala ya kawo mana sauki da sassauci, idan budurwa ce ki roki Allah ya kawo miki miji nagari, haka nan saurayi shi ma ya roki Allah ya kawo masa mata ta gari.

A takaice, wannan shi ne jan hankalina da fatan Allah ya sa za mu sa ido yadda ya kamata, Allah ya sa mu dace, amin.

Rayuwa
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Talauci Ba Hujjar Aikata Muggan Laifukka Ba Ne 

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Marurun Zuciya

2027: Bukatar Zaben Shugabanni Na Gari

May 10, 2026
Next Post
Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (4)

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (4)

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.