• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani lamari mai kamar wasan kwaikwayo da ya faru a karamar hukumar Rano ta jihar Kano bayan wata mata mai suna Malama Khadija ta kashe aurenta ta auri saurayin ‘yarta. 

Lamarin ya faru ne bayan diyar mai suna A’isha ta ki amincewa da mai neman aurenta, inda mahaifiyar ta ce, auran mai neman ‘yarta bai haramta ba a Musulunci.

  • An Gudanar Da Baje Kolin Hotunan Tashar Samaniya Ta Sin

Tun da farko dai ‘yan uwan matar sun shaida wa gidan rediyon Freedom cewa suna zargin kwamandan Hisbah na karamar hukumar Rano da aurar da ‘yarsu ba tare da izininsu ba, kuma ba su ma san inda take ba.

 

Sai dai kuma da take magana da Freedom Radio, Malama Khadija ta ce tana cikin koshin lafiya kuma tana zaune lafiya da sabon mijin nata.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Ta bayyana cewa bayan da ta fahimci cewa ’yarta ta yanke shawarar ba za ta auri mutumin ba, sai ta ji bai kamata su biyu su rasa shi ba, don haka ta yanke shawarar auran mutumin. Ta kuma kara da cewa itama tana da kyau kamar ‘yarta.

 

Ta ce, “Ban yi auran cikin jahilci ba. Na tuntubi malamai suka ce hakan ba haramun ba ne. Da na tuntubi mutumin kan aure na, ya amince shi amma iyayena da ’yan uwana sun ki amincewa da auran. Hakan ne ya sa na yanke shawarar zuwa Hisbah su daura mana aure wanda yanzu haka, muna cikin farin ciki.”

Kawun Malama Khadija, Abdullahi Musa Rano, ya ce sun ki yarda ta auri mutumin ne sabida da gangan ta kashe aurenta na farko domin ta auri mai neman ‘yarta.

 

Ya bayyana cewa, “Ta matsa wa mijinta ya sake ta don kawai ta auri wannan sabon mijin na ta. Ba za mu yarda da wannan abin kunyar ba a cikin danginmu. Wannan shine dalilin da ya sa muka ki hada su da aure. Ba mu ji dadin abin da Hisbah ta yi ba, kuma muna ba da rahoton neman ‘yar mu. Muna son babban kwamanda da gwamnatin jihar su shiga cikin wannan lamarin.”

 

Da aka tuntubi kwamandan Hisbah, Ustaz Nura Rano, ya ce hukumar ta jiha ce kadai ke da damar yin magana kan lamarin.

 

Da aka tuntubi babban kwamandan Hisbah na jihar, Sheikh Harun Ibn-Sina, ya yi alkawarin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Daga Daily trust


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zan Tabbatar Da Hadin Kan Nijeriya Da Kubutar Da Ita Daga Halin Da Muke Ciki —Atiku

Next Post

Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

1 hour ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

2 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

4 hours ago
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

7 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

8 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

10 hours ago
Next Post
Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.