ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano

by Sulaiman
4 years ago
Mata

Wani lamari mai kamar wasan kwaikwayo da ya faru a karamar hukumar Rano ta jihar Kano bayan wata mata mai suna Malama Khadija ta kashe aurenta ta auri saurayin ‘yarta. 

Lamarin ya faru ne bayan diyar mai suna A’isha ta ki amincewa da mai neman aurenta, inda mahaifiyar ta ce, auran mai neman ‘yarta bai haramta ba a Musulunci.

  • An Gudanar Da Baje Kolin Hotunan Tashar Samaniya Ta Sin

Tun da farko dai ‘yan uwan matar sun shaida wa gidan rediyon Freedom cewa suna zargin kwamandan Hisbah na karamar hukumar Rano da aurar da ‘yarsu ba tare da izininsu ba, kuma ba su ma san inda take ba.

ADVERTISEMENT

 

Sai dai kuma da take magana da Freedom Radio, Malama Khadija ta ce tana cikin koshin lafiya kuma tana zaune lafiya da sabon mijin nata.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ta bayyana cewa bayan da ta fahimci cewa ’yarta ta yanke shawarar ba za ta auri mutumin ba, sai ta ji bai kamata su biyu su rasa shi ba, don haka ta yanke shawarar auran mutumin. Ta kuma kara da cewa itama tana da kyau kamar ‘yarta.

 

Ta ce, “Ban yi auran cikin jahilci ba. Na tuntubi malamai suka ce hakan ba haramun ba ne. Da na tuntubi mutumin kan aure na, ya amince shi amma iyayena da ’yan uwana sun ki amincewa da auran. Hakan ne ya sa na yanke shawarar zuwa Hisbah su daura mana aure wanda yanzu haka, muna cikin farin ciki.”

Kawun Malama Khadija, Abdullahi Musa Rano, ya ce sun ki yarda ta auri mutumin ne sabida da gangan ta kashe aurenta na farko domin ta auri mai neman ‘yarta.

 

Ya bayyana cewa, “Ta matsa wa mijinta ya sake ta don kawai ta auri wannan sabon mijin na ta. Ba za mu yarda da wannan abin kunyar ba a cikin danginmu. Wannan shine dalilin da ya sa muka ki hada su da aure. Ba mu ji dadin abin da Hisbah ta yi ba, kuma muna ba da rahoton neman ‘yar mu. Muna son babban kwamanda da gwamnatin jihar su shiga cikin wannan lamarin.”

 

Da aka tuntubi kwamandan Hisbah, Ustaz Nura Rano, ya ce hukumar ta jiha ce kadai ke da damar yin magana kan lamarin.

 

Da aka tuntubi babban kwamandan Hisbah na jihar, Sheikh Harun Ibn-Sina, ya yi alkawarin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Daga Daily trust

Mata
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.