• Leadership Hausa
Thursday, February 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano

by Sulaiman
1 week ago
in Labarai
0
Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano

Wani lamari mai kamar wasan kwaikwayo da ya faru a karamar hukumar Rano ta jihar Kano bayan wata mata mai suna Malama Khadija ta kashe aurenta ta auri saurayin ‘yarta. 

Lamarin ya faru ne bayan diyar mai suna A’isha ta ki amincewa da mai neman aurenta, inda mahaifiyar ta ce, auran mai neman ‘yarta bai haramta ba a Musulunci.

  • An Gudanar Da Baje Kolin Hotunan Tashar Samaniya Ta Sin

Tun da farko dai ‘yan uwan matar sun shaida wa gidan rediyon Freedom cewa suna zargin kwamandan Hisbah na karamar hukumar Rano da aurar da ‘yarsu ba tare da izininsu ba, kuma ba su ma san inda take ba.

 

Sai dai kuma da take magana da Freedom Radio, Malama Khadija ta ce tana cikin koshin lafiya kuma tana zaune lafiya da sabon mijin nata.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Sace A Kaduna 

Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil

Ta bayyana cewa bayan da ta fahimci cewa ’yarta ta yanke shawarar ba za ta auri mutumin ba, sai ta ji bai kamata su biyu su rasa shi ba, don haka ta yanke shawarar auran mutumin. Ta kuma kara da cewa itama tana da kyau kamar ‘yarta.

 

Ta ce, “Ban yi auran cikin jahilci ba. Na tuntubi malamai suka ce hakan ba haramun ba ne. Da na tuntubi mutumin kan aure na, ya amince shi amma iyayena da ’yan uwana sun ki amincewa da auran. Hakan ne ya sa na yanke shawarar zuwa Hisbah su daura mana aure wanda yanzu haka, muna cikin farin ciki.”

Kawun Malama Khadija, Abdullahi Musa Rano, ya ce sun ki yarda ta auri mutumin ne sabida da gangan ta kashe aurenta na farko domin ta auri mai neman ‘yarta.

 

Ya bayyana cewa, “Ta matsa wa mijinta ya sake ta don kawai ta auri wannan sabon mijin na ta. Ba za mu yarda da wannan abin kunyar ba a cikin danginmu. Wannan shine dalilin da ya sa muka ki hada su da aure. Ba mu ji dadin abin da Hisbah ta yi ba, kuma muna ba da rahoton neman ‘yar mu. Muna son babban kwamanda da gwamnatin jihar su shiga cikin wannan lamarin.”

 

Da aka tuntubi kwamandan Hisbah, Ustaz Nura Rano, ya ce hukumar ta jiha ce kadai ke da damar yin magana kan lamarin.

 

Da aka tuntubi babban kwamandan Hisbah na jihar, Sheikh Harun Ibn-Sina, ya yi alkawarin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Daga Daily trust

Previous Post

Zan Tabbatar Da Hadin Kan Nijeriya Da Kubutar Da Ita Daga Halin Da Muke Ciki —Atiku

Next Post

Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

Related

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Sace  A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Sace A Kaduna 

49 mins ago
Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil
Kananan Labarai

Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil

1 hour ago
Gini Ya Rufta, Ya Kashe Mutane, Da Dama Sun Jikkata A Abuja
Manyan Labarai

Gini Ya Rufta, Ya Kashe Mutane, Da Dama Sun Jikkata A Abuja

2 hours ago
Ƙungiyar Marubuta Ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Mahmoon Baba-Ahmed
Labarai

Ƙungiyar Marubuta Ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Mahmoon Baba-Ahmed

2 hours ago
CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin       
Manyan Labarai

CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin      

3 hours ago
Hisbah Ta Wanke Matar Da Ta Auri Saurayin ‘Yarta A Jihar Kano
Manyan Labarai

Hisbah Ta Wanke Matar Da Ta Auri Saurayin ‘Yarta A Jihar Kano

4 hours ago
Next Post
Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

Dino Melaye Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Taron PDP Yayin Da Yake Zolayar Tinubu

LABARAI MASU NASABA

An Samu Sabbin Nasarori A Hadin Gwiwar Cinikayya Da Tattalin Arziki Karkashin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

An Samu Sabbin Nasarori A Hadin Gwiwar Cinikayya Da Tattalin Arziki Karkashin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

February 2, 2023
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Sace  A Kaduna 

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Sace A Kaduna 

February 2, 2023
Sin: Ya Kamata A Rika Girmama Akidun Mabiya Addinin Musulunci

Sin: Ya Kamata A Rika Girmama Akidun Mabiya Addinin Musulunci

February 2, 2023
Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil

Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil

February 2, 2023
An Fara Aiki Da Cibiyar Bayanai Ta Kano

An Fara Aiki Da Cibiyar Bayanai Ta Kano

February 2, 2023
Gini Ya Rufta, Ya Kashe Mutane, Da Dama Sun Jikkata A Abuja

Gini Ya Rufta, Ya Kashe Mutane, Da Dama Sun Jikkata A Abuja

February 2, 2023
Ƙungiyar Marubuta Ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Mahmoon Baba-Ahmed

Ƙungiyar Marubuta Ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Mahmoon Baba-Ahmed

February 2, 2023
Har Yanzu Ana Kuka Sakamakon Yadda ‘Yan Sandan Amurka Ke Nuna Karfin Tuwo

Har Yanzu Ana Kuka Sakamakon Yadda ‘Yan Sandan Amurka Ke Nuna Karfin Tuwo

February 2, 2023
CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin       

CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin      

February 2, 2023
Sabon Kwamitin Lura Da Takara Da Sin Da Amurka Ta Kafa Ba Zai Haifar Da Dan Mai Ido Ba

Sabon Kwamitin Lura Da Takara Da Sin Da Amurka Ta Kafa Ba Zai Haifar Da Dan Mai Ido Ba

February 2, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.